Khalifa Bashir Sheikh Musa Kallah na mika godiyarsa da kuma ban gajiya amadadin iyalai da kuma dukkanin almajiran zawiyyarsa ga darirruwan jama’a da suka halarcci daurinauren dan sa.

Daurin auren wanda aka gabatar a masallacin Alfukan, anyi shine  ranar Jumaar da ta gabata  bayan sallar Jumaa.

Mutane da dama daga farni farni na rayuwar al’umma suka halarci wajen daurin auren kuma suka sa albarka.

Ko shakka babu anga taron mutanen kasashen waje, mayan malamai, manyan yan boko, manyan yan siyasa da kuma jami’en tsaro da kuma darirruwan mutane a wajen dauren auren.

Anga halartar dukkanin mambobin majilasar Shura  na Darikar Attijaniya, wakilan ofisoshin jakadanci na kasashen Sudan, Niger, Lebanon da Tunis a  wajen daurin auren. Haka kuma akwai manyan yan kasuwa, manyan malamai da kum yan siyasa.

Babu tambaya, daga ganin fuskar uban ango, Khalifa Bashir Sheikh Musa Kallah, kasan tana cike da farin ciki wanda ba zai zaiyanuba domin bakinsa a bude yake saboda murnar ganin tururruwar dan adam da suka amsa gayyatarsa. 

Fatanmu Allah yasa albarka.

By Sani Yusif

I was at the production unit of the Triumph Publishing Company, Kano but my keen interest in sports journalism made me to be sports writer and maintained a sports column called (Sports Eye) after my mentor Sani Muhammad Zaria transferred his service to New Nigeria newspapers in Kaduna. And when the government closed the Triumph in 2012, I was transfered to lectured DTP in the Department of Printing Technology of Kano State Polytechnic. And now that I retired, i used to visit the institution weekends for part-time lecturing.