Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Nigeria’s Sports Tourism takes center stage …as NASTOCE 2026 launches in Abuja

      February 8, 2026

      Kano’s Gwadabe, four others for FIFA’s course in Kigali

      February 5, 2026

      Barau FC breaks new ground with Pre-Kick-off bonus payment

      February 4, 2026

      Adamu clinches landslide victory as Lady Captain of TYB Golf Club

      February 1, 2026

      Novelty football match: Kurmawa inmates overpower NDLEA’s Marwa’s Boys

      January 29, 2026
    • Column

      NPFL Under Fire: Governance, sanctions with fight for transparency

      February 9, 2026

      Sportyseye in prison: Lifetime experience of agony and joy

      February 2, 2026

      Amidst friends, family, others: Chairman Gwadabe’s daughter Ameera weds

      January 26, 2026

      In defence of BUA’s Super Eagles largess

      January 19, 2026

      Changes needed in Kano State Sports Commission

      January 12, 2026
    • News & Media

      Kano Football Coaches host Modern Coaching Seminar for members

      January 7, 2026

      Oseni replaces Ramat as NERC chairman after Senate rejection

      December 19, 2025

      Ahned Musa: Honoring 15 Years of Dedication and Selfless Service

      December 17, 2025

      2025 CIPPON Annual General Meeting (AGM) to Hold in Kano

      November 22, 2025

      Congregation Election: ADUSTECH’s NASU, SSANU candidates triumph

      November 18, 2025
    • Analysis

      Memo to KNSG’s committee on Kano Pillars’ performance

      February 9, 2026

      Re-Calls on Gov. Yusuf to Dissolve Kano Pillars Board, but retain GM Musa

      February 6, 2026

      Kano Pillars and Sports Commission: Story of Dwindling Fortunes

      February 5, 2026

      Jan kafar Pillars wajen ɗaukar sababbin ’yan wasa: Me ke faruwa?

      February 4, 2026

      Gaskiyar banbanci tsakanin Kano Pillars da Barau FC

      February 4, 2026
    • Personality Profiles

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Gaskiyar banbanci tsakanin Kano Pillars da Barau FC
    Sports Analysis

    Gaskiyar banbanci tsakanin Kano Pillars da Barau FC

    Sani YusifBy Sani YusifFebruary 4, 2026
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    logo

    Sau da dama, wasu marubuta da masu sharhi, har da wasu daga cikin abokan aikinmu, kan kasa bambance a fili tsakanin kungiyar Kano Pillars da takwararta ta Barau FC.

    A mafi yawan lokuta, yayin da suke yin sharhi, suna bayyana mamaki kan yadda shugabannin Kano Pillars suka kasa kwaikwayon salo ko dabarun da Barau FC ta yi amfani da su wajen fita daga halin kunci da ta tsinci kanta a baya-bayan nan.

    Abin da suke mantawa da shi shi ne, kungiyar Barau FC ba ta kama da Kano Pillars ba wajen tsarin mallaka da tafiyar da al’amura har da gudanarwa.

    Barau FC kungiya ce mallakar mutum guda, yayin da Kano Pillars kuma mallakar gwamnati ce.

    Wannan bambanci ne babba. A Barau FC, abubuwa na tafiya da sauri saboda babu dogon tsari na gwamnati.

    Idan ana bukatar yanke hukunci ko aiwatar da wani abu, waya daya kacal na iya warware komai. Amma a Kano Pillars ba haka lamarin yake ba.

    Idan muka duba sosai, za mu ga yadda Barau FC ta iya sallamar ‘yan wasa da dama lokaci guda tare da daukar sabbi ba tare da wata tangarda ba, saboda babu abin da ake kira bureaucratic bottleneck a cikinta.

    Haka kuma, lokacin da aka samu sabani tsakanin kungiyar da tsohon shugaban ta tare da wasu mukarrabansa, an sallame su nan take tare da biyansu hakkokinsu domin rage radadin rabuwa.

    Duk wadannan abubuwa ba za su yi sauki a Kano Pillars ba. Duk wani mataki sai ya bi tsari daga Ma’aikatar Wasanni, zuwa ofishin Sakataren Gwamnati, sannan har zuwa ofishin Mai Girma Gwamna domin neman sahalewa.

    Bugu da kari, gwamnati na da cikakken bayanai kan duk wanda ke yi wa Kano Pillars hidima, tare da biyansu albashi ko alawus ta tsarin payroll na gwamnati ko wani tsari dabam.

    Don haka ba zai yiwu mutum guda ya mike tsaye ya sallami kowa ba tare da bin ka’ida ba, kamar yadda ake iya yi a Barau FC.

    A takaice, Barau FC kamar kasuwancin mutum guda ne (one-man business), yayin da Kano Pillars kuma kungiya ce ta jama’a (public institution).

    Ba a taba jin shugaban kamfani ko wata ma’aikatar gwamnati ya kori ma’aikata lokaci guda ba tare da bin doka ba. Amma a kungiya irin ta Barau, hakan abu ne mai sauki.

    Saboda haka, ya dace masu sharhi da marubuta su kara zurfafa bincike domin fahimtar wadannan bambance-bambance kafin su rika kwatanta kungiyoyin biyu.

    Gaskiyar bambamci Pillars da Barau tsakanin
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleBarau FC breaks new ground with Pre-Kick-off bonus payment
    Next Article Jan kafar Pillars wajen ɗaukar sababbin ’yan wasa: Me ke faruwa?
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Memo to KNSG’s committee on Kano Pillars’ performance

    February 9, 2026

    Re-Calls on Gov. Yusuf to Dissolve Kano Pillars Board, but retain GM Musa

    February 6, 2026

    Kano Pillars and Sports Commission: Story of Dwindling Fortunes

    February 5, 2026

    Jan kafar Pillars wajen ɗaukar sababbin ’yan wasa: Me ke faruwa?

    February 4, 2026

    As Pillars Return to SAS: What I expect from fans & management

    December 23, 2025

    My Sports Agenda for North-West Development Commission

    December 15, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Memo to KNSG’s committee on Kano Pillars’ performance

    February 9, 2026

    NPFL Under Fire: Governance, sanctions with fight for transparency

    February 9, 2026

    Nigeria’s Sports Tourism takes center stage …as NASTOCE 2026 launches in Abuja

    February 8, 2026

    Re-Calls on Gov. Yusuf to Dissolve Kano Pillars Board, but retain GM Musa

    February 6, 2026

    Kano’s Gwadabe, four others for FIFA’s course in Kigali

    February 5, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.