Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Inferno: Mai Samba mourn Singer Market fire victim

      February 16, 2026

      Nigeria’s Sports Tourism takes center stage …as NASTOCE 2026 launches in Abuja

      February 8, 2026

      Kano’s Gwadabe, four others for FIFA’s course in Kigali

      February 5, 2026

      Barau FC breaks new ground with Pre-Kick-off bonus payment

      February 4, 2026

      Adamu clinches landslide victory as Lady Captain of TYB Golf Club

      February 1, 2026
    • Column

      Pandemonium: As NPFL matches turn into War Zones

      February 16, 2026

      NPFL Under Fire: Governance, sanctions with fight for transparency

      February 9, 2026

      Sportyseye in prison: Lifetime experience of agony and joy

      February 2, 2026

      Amidst friends, family, others: Chairman Gwadabe’s daughter Ameera weds

      January 26, 2026

      In defence of BUA’s Super Eagles largess

      January 19, 2026
    • News & Media

      Kano Football Coaches host Modern Coaching Seminar for members

      January 7, 2026

      Oseni replaces Ramat as NERC chairman after Senate rejection

      December 19, 2025

      Ahned Musa: Honoring 15 Years of Dedication and Selfless Service

      December 17, 2025

      2025 CIPPON Annual General Meeting (AGM) to Hold in Kano

      November 22, 2025

      Congregation Election: ADUSTECH’s NASU, SSANU candidates triumph

      November 18, 2025
    • Analysis

      Memo to KNSG’s committee on Kano Pillars’ performance

      February 9, 2026

      Re-Calls on Gov. Yusuf to Dissolve Kano Pillars Board, but retain GM Musa

      February 6, 2026

      Kano Pillars and Sports Commission: Story of Dwindling Fortunes

      February 5, 2026

      Jan kafar Pillars wajen ɗaukar sababbin ’yan wasa: Me ke faruwa?

      February 4, 2026

      Gaskiyar banbanci tsakanin Kano Pillars da Barau FC

      February 4, 2026
    • Personality Profiles

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Hira ta musamman da akai tareda Kano Golf Club Captain, Ambassada Ali M. Magashi.
    Sports News

    Hira ta musamman da akai tareda Kano Golf Club Captain, Ambassada Ali M. Magashi.

    Sani YusifBy Sani YusifFebruary 2, 2024
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram

    Daga Jamilu Uba Adamu

    Tambaya : Ranka ya daɗe barkammu da warhaka, ranka ya daɗe za mu so mu ɗan ji ƙaramin tarihinka misali abinda ya shafi ma harkar wasannin golf da ya aka yi aka fara? Mai sauraro zai so ya ji wannan.

    Ambassador : To jama’a Assalamu alaikum am…. wasan golf dai na fara shi ina jin yau shekara wajen goma sha biyu ko sha uku. Dalilin da ya sa kuma na fara golf, da ƙwallo nake yi har bayan na girma. akwai inda muke buga ƙwallo a nan Turona da kuma bayan Saudi Embassy, muna zuwa kowanne juma’a da Asabar da Lahadi muna buga ƙwallon ƙafa, sai na zo na ji ciwo da filin sukuwa da na ji ciwo, daga ƙwallon ƙafa sai na bar ƙwallon ƙafa sai na koma squash. ina squash shi ma na zo na yi hatsari a gurin squash na faɗi sai na bar squash. Sai na ce to tunda girma ya zo ya kamata na koma wasan da…. da wahala dai in ba tsautsayi ba a ji ciwo sai na je na fara golf. So ka ji dalilin fara golf ɗina, na yi wajen shekara 13 kenan.

    Tambaya : Masha’allah ranka ya daɗe. To yanzu ga shi a gasar golf ɗin nan a cikin wannan golf ɗin da kake bugawa ga shi kuma har Allah Ubangiji ya sa ka zama shugaba ko Captain na Kano club, me za ka faɗa game wannan matsayi da Allah ya ba ka?

    Ambassador : To shugabanci ka san shi na Allah ne. Ka san Allah shi yake zaɓar shugabanni. Kuma a duk inda aka haɗu aka yi tarayya, ya kamata a samu shugabanci domin a samu tsari. A, shigata na farko na shugabancin Kano Club na fara da PRO, yau ina jin ya kai shekara 10 da na yi PRO. Bayan na yi PRO yau shekara huɗu baya da suka wuce aka zaɓe ni a Captain. To ina Captain sai aka naɗa ni ambassador sai na bar ƙasa. To kuma yanzu da na gama aikina na dawo, har yanzu sai na zo na tadda an sake yin zaɓe, an zaɓe ni captain. Wannan girma ne na Ubangiji sai dai mu yi masa godiya kuma mu roƙe shi a kan ya yi mana jagora yanda za mu yi wannan abin a cikin tsari da kuma adalci.

    Tambaya : Masha’allah ga gasa wacce za a fara in Allah ya kai mu ranar Juma’a zuwa ranar Lahadi. Me wannan gasa, me za ka faɗa game da wannan gasa da za a gabatar da ita a nan Kano?

    Ambassador : To wannan gasa gagarumar gasa ce, dama al’ada ce shi filin golf duk lokacin da aka yi zaɓen sabon shugaba wato captain, dole ne yakan yi wasa na buɗe share fagen mulkinsa. So a wannan lokacin shi ne ake kira captain’s day. To tunda ina da abokanan hulɗa da abokanan wasa a dukka ƙasar nan da ma duniya bakiɗaya. Wannan wasa akwai mutane da yawa don a yanzu haka muna da wajen sama da mutum 200 da suka yi rajista daga nan kuma muna ga daga nan zuwa Asabar da wanda za su yi rajista a fili za mu samu ‘yan wasa sun kai 250, muna da ‘yan wasa na Kano da muka saba wasa da su, muna da ‘yan wasan Kaduna, Abuja, Katsina, Bauchi, muna da ‘yan Legas da yawa da za su zo. Har da ma abokanan wasana daga Korea, akwai waɗanda za su zo. Akwai kuma abokan wasana daga America su ma da za su zo. So, gagarumin taro ne za mu yi, za a yi kwana biyu ana wannan wasa, kuma mun gayyaci shuwagabannin da dama, da ministan wasa da ministan ƙasashen waje, da minstan al’adu na gargajiya da kuma gwamnoninmu na Kano, Jigawa da Katsina, duka mun gayyace su. Kuma wasu daga cikinsu gwamnoni guda biyu sun ba da answer cewa za su zo kuma ministoci guda biyu sun ba da answer suna zuwa.

    Tambaya: Masha’allah, Captain Ali Magashi, wane fata za ka yi wa masu harkokin wasannin sanda na golf a ƙarshe ?

    Ambassador : To shi wasan golf wasa ne wanda za ka iya fara shi kana shekara huɗu na haihuwa, kuma za ka iya fara shi kana shekara tamanin. So wasa ne wanda shi ya fi komai sauki, kuma wasa ne wanda zai motsa maka jiki duka jikinka gabakiɗaya, kuma ya motsa maka ƙwaƙwalwarka. To saboda haka, wasa ne da nake kiran mutanen Kano gabakiɗaya da kewaye a zo a shiga cikin wannan wasa. Kuma a yanzu yadda wasanni suka zama, sun zama hanyar samun kuɗi ga matasa. Ina kiran matasanmu su zo su shiga wannan wasa tunda yau babu ɗan wasanni a duniya da ake biya kamar ‘yan golf, saboda a yau kana jin sunan Tiger Boot, yana da sama da Dala biliyan ɗaya ta Amurka, kuma dukka a harkar golf ɗin nan ya same ta. So ka ga idan muka tabbatar yaranmu sun shiga wannan harka, to zai bunƙasa tattalin arziƙi namu kuma zai kawo lafiya a zamanmu. Kuma shi wannan fili namu mai tarihi da yawa shi ne fili na farko a ƙasar Afrika ta yamma tun zuwan Turawa ba ma Nigeria ba, tun zuwan Turawa Kano 1903 da suka zo suka ɗauki wannan fili abinda suke kira Kano protectorate suka zagaye tun daga kan Central Hotel in ka zaga ka tafi har ka je gidan Ɗan Hausa ka zagayo gidan gwamna ka tafi ka haɗa da Giginyu da Badawa ka je har Tudun Wada ka gangaro ka zagayo zuwa gidan Gwamna Shekarau har ka taho zuwa inda Nepa take Miller Road take ka shigo ka zo kan Kano Club duk su Daula su Welcare duka suna cikin wannan abu. To a girman garin Kano da ya zo an fitar da tituna an yi menene da yawa filin ya ragu sai abin da ya yi saura. To muna son mu nuna wa duniya cewa wannan fili ne na tarihi da yawa. Kuma muna son gwamnatin tarayya ta ɗauki wannan fili ta maida shi abinda ake kira nationl heritage, yadda duk duniya idan aka zo mutane za su so su san fili na farko a Nigeria za zo su yi wasa duk a kansa. To wannan zai ƙara abinda ake kira ƙarfin “tourism” a Kano. zai sa mutane da yawa su rinƙa zuwa kano saboda tarihin wannan fili idan aka gyara shi ya zo ya zama standard. To babban abin da ya sa muka haɗa wannan gagarumin taron shi ne, mu buɗe wa mutane ido a sanar da duniya cewa shi ainahin wasan nan ma a Nigeria a Kano aka fara shi, kuma mutanen Kano su san muhimmancinsa, mutanen Nigeria su san muhimmancin Kano a kan wannan harka. Kuma a sa mai ido yadda za a ci gaba da tattalin shi wannan fili ba tare da ko wata gwamnati ba ta zo da niyyar ta ce za ta karɓe fili. Saboda a yanzu wannan fili ne na wasanni ka ga bai kamata ba a ce kowanne shekara sai an caji crown trend da tournament trade da land use charges da yawa da ake yi. Ya kamata a ce gwamnati ta taimaka, to idan gwamnatin tarayya ta dauke shi, ka ga duka wannan nauyi zai ɗauke kuma za a samu hanyar da za a gyara shi.

    Ambasada mun gode ƙwarai

    Hira musamman Ta
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleAdo Salisu’s daughter’s wedding: How Kano SWAN spoilsport my day
    Next Article CNS swimming tourney:  Delta Police Command shines…As ACP S. Bello receives award
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Inferno: Mai Samba mourn Singer Market fire victim

    February 16, 2026

    Nigeria’s Sports Tourism takes center stage …as NASTOCE 2026 launches in Abuja

    February 8, 2026

    Kano’s Gwadabe, four others for FIFA’s course in Kigali

    February 5, 2026

    Barau FC breaks new ground with Pre-Kick-off bonus payment

    February 4, 2026

    Adamu clinches landslide victory as Lady Captain of TYB Golf Club

    February 1, 2026

    Novelty football match: Kurmawa inmates overpower NDLEA’s Marwa’s Boys

    January 29, 2026
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Inferno: Mai Samba mourn Singer Market fire victim

    February 16, 2026

    Pandemonium: As NPFL matches turn into War Zones

    February 16, 2026

    Memo to KNSG’s committee on Kano Pillars’ performance

    February 9, 2026

    NPFL Under Fire: Governance, sanctions with fight for transparency

    February 9, 2026

    Nigeria’s Sports Tourism takes center stage …as NASTOCE 2026 launches in Abuja

    February 8, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.