Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Kungiyar Barau: Kuskuren da Ibrahim Canji, mabiyansa suka tafka

      September 30, 2025

      Sauye-sayen kungiyar Barau: Kuskuren Sanata Barau tare dana Canji

      September 25, 2025

      Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

      September 9, 2025

      Gumel, Maizare, others to head newly formed SPS

      August 29, 2025

      Youth Games: For Kano Contingent’s Airs trip, kudos to Gov Abba

      August 27, 2025
    • Column

      SWAN: Genuine sports stakeholder than NFF, other federation members

      October 6, 2025

      Changes in Barau FC: Where DSP Barau Jibrin fumbles

      September 29, 2025

      Shehu Dikko one year in office: Is there light in the tunnel?

      September 22, 2025

      Eagles’ World Cup elimination: Gusau, his associates ought to go

      September 15, 2025

      Sports Develpt in Kano: What Gov Abba should do

      September 8, 2025
    • News & Media

      Re-Extortion at Urology Center: Gov Abba must hear this

      October 10, 2025

      Environmental Journalists begin two-day training in Abuja

      September 23, 2025

      Two-day training for environment journalists in Abuja

      September 21, 2025

      To transform smart living in Nigeria: FENAC secure solutions, collaborates with South African firm

      September 17, 2025

      Re-Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

      September 11, 2025
    • Analysis

      Rashin kokarin Kano Pillars da Barau: Sai fa gwamnati ta yi wani abu

      October 7, 2025

      Barau FC, please wake up.

      September 15, 2025

      Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

      September 9, 2025

      NPFL matches: Gov Abba backs Barau FC, shames pessimists

      August 23, 2025

      Eunice Chike must be incorporated into Nigeria’s football system immediately

      August 4, 2025
    • Personality Profiles

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024

      Dr. Usman Ibrahim Aikawa: New Kano Poly, Director Academic Planning

      January 2, 2024
    Sports Eye
    Home » Kungiyar Barau: Kuskuren da Ibrahim Canji, mabiyansa suka tafka
    Sports News

    Kungiyar Barau: Kuskuren da Ibrahim Canji, mabiyansa suka tafka

    Sani YusifBy Sani YusifSeptember 30, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    1b

    Ana wata ga wata, domin a daidai lokacin da kungiyar kwallon kafa ta Barau ta bankado wasu almindahanonin kudi masu nauyi da ake ta tafkawa a kungiyar wanda kuma ake zargin shugabancin Ibrahim Shitu Canji yakeyi, sai gashi Ibrahim Canji na nuna wasu halaye ga kungiyar wadanda basu kamata ba ko kadan.

    Wata majiya mai tushi ta shedawa wannan kafa cewa tun lokacin da aka bankado almindahanonin zabtarewa yan wasan kungiyar Barau kusan rabin albashinsu yasa mamallakin kungiyar, Sanata Barau Jibrin Maliya ya umarci da gabatar da canje-canje a tsarin shugabancin kungiyar.

    Yin binciken ke da wuya aka bankado wani abu mara dadinji, watau yadda ake zabtarewa wasu daga cikin yan wasan kungiyar Barau din rabin albashinsu ba gaira ba dalilin kuma babu dalilin yin hakan.

    Haka kuma rashin samun nasarar kungiyar ta Barau a wasannin da ta buga guda hudu duk da makudankudin da ake kashewa kungiyan ya bayyana rashin kwarewa da gogewar shugabancin Ibrahim Shitu Canji a harkar wanda shima ya taimaka wajen samarda canje-canjen a kungiyar Barau din.

    Hakika canje-canjen  wanda ya kawo wasu mutum biyu masu kwarewa da ilmin abin ya ragewa shi Ibrahim Shitu Canji karfin fada a ji a kungiyar sosai, abinda ake ganin shi ya hasala shi.

    Shi wannan canje-canjen ya shigo da tsohon shugaban kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, Alhaji Kabiru Baita, a matsayin maitaimakin shugaba da kuma Dominik Yofa, tsohon shugaban kungiyar kwallon kafa ta Lobi dake jihar Binuwe, a matsayin babban manajan kungiyar kwallon kafa ta Barau.

    Ko shakka babu wata majiya ta tabbatarwa wannan kafa cewa wannan al’amarin baiyiwa Ibrahim Canji dadi ba domin a da shine ke da wuka kuma shine da nama domin Sanata Barau ya bar masa komai a hannunsa.

    Amma kash, a maimakon shugabancin Ibrahim Canji yayi abinda yakamata, sai a wata majiya suka kawo son zuciya wanda baiyiwa shi Sanata Barau da kungiyar dadi ba wanda ya jawo samarda wani tsari da zai shigo da wasu don daidaita al’amarin.

    Hakika shigowar wannan mutum biyun watau Baita da Dominik cikin tsarin shugabancin kungiyar baiyiwa Ibrahim Canji dadi ba domin ya rage masa kafin fada aji a cikin kungiyar da yake tunkaho shine ruhinta a jihar Kano.

    Wani bincike ya nuna cewa tun shigowa da kuma kama aikin wadanda mutum biyun, watau Kabiru Baita da kuma Dominik Yofa, Ibrahin Canji ya canja salo da kuma ta yin guna guni da kuma nuna halin ni ‘yasu.

    Fara nuna halaye marasa kyau da Ibrahim Canji yakeyi a harkokin kungiyar sai fitowa fili sukeyi kullum, domin ko tafiya zuwa wasan kungiyar da tayi da kungiyar Kun Khalifa bai jeba kuma baaga keyarsa a wajen haduwa don tafiya wasan ba.

    Wata majiyar ta tabbatarwa wannan kafa cewa kafin tafiyar kungiyar Barau zuwa wancen wasannata da kungiyar Kun Khalifa, an jira kuma, an kuma nemi shi Ibrahim Canji amma ba’aganshi ba kuma ba’aji daga gareshiba.

    Kuma a lokacin da aka nemeshi ta lambobin wayoyinsa shima baayi nasarar saminshiba domin dukkanninsu a rufe suke.

    Haka aka hakura aka tafi filin jirgin sama na Malam Aminu Kano don shiga jirgin sama aka kuma tafi kuma aka sami nasara ba Ibrahim Shitu Canji ba mukarrabensa. Wannan ba karamin kuskure bane domin ita maganar almindahana bafa fito da ita akayi ba har izuwa wnnan lokacin abin a cikin zargi yake.

    Bincike ya nuna cewa dukkannin makarraben Ibrahim Canji dake rike da wani mikami a kungiyar kamarsu Yahaya Muhammad, daraktan wasannin kungiyar, Jabir Hassan, Technical Consultant, Abubakar Sadiq, mai kula da bangaren kasuwancin kungiyar, Umar Lawan wanda shine sakatare da kuma Isma’il Mahmoud, mai kula da walwala da jin dadin kungiyar sun juyawa kungiyar baya domin nuna biyayyarsu ga Ibrahim Canji saboda kin bin kungiyar zuwa wasanta da Kun Khalifa.

    Hakika rashin zuwansu Ibrahim Canji da mukarrabensa baiyi wani tasiri ba domin a maimakon samun rashin nasara, kungiyar Barau samun nasararta ta farko tayi a kan masu masaukinsu.

    Sai dai wata kafa ta bayyana mana cewa wannan rashin kyautawa da Canji da mukarrabensa sukayi bazai musu dadi ba domin kungiyar na iya tunanin ladaftar dasu.

    Wannan kafa tana kira ga Ibrahim Canji da ya mukarrabensa da su canja tunani domin ita rayuwa juyawa takeyi. Ko da baa samesu laifin komi ba, bawanda zaita kasha kudinsa akan kungiya wadda ba nasara kuma ya tsaya yana kallo. Dole yayi wani abu ko hobbasa da zai kawo gyara.

    A ganinmu Ibrahim Canji da mukarrabensa godewa Allah da kuma mai kungiyar yakamata suyi ba tawaye ba, domin laifin da ake zarginsu babbane kuma tunda bai fallasa ba, sai suyi shiru kuma su gyara ba yin tawaye ba.

    Su sani fa, anayi da kai…

    Canji da Ibrahim kungiyar Barau Kuskuren ya tafka
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleChanges in Barau FC: Where DSP Barau Jibrin fumbles
    Next Article SWAN: Genuine sports stakeholder than NFF, other federation members
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Sauye-sayen kungiyar Barau: Kuskuren Sanata Barau tare dana Canji

    September 25, 2025

    Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

    September 9, 2025

    Gumel, Maizare, others to head newly formed SPS

    August 29, 2025

    Youth Games: For Kano Contingent’s Airs trip, kudos to Gov Abba

    August 27, 2025

    Tataburzar Barau da hukumar wasanni: Yakamata gwamna Abba ya tsawata

    August 18, 2025

    Kano Coaches welcome Bosso back to Kano as he takes up Barau’s TA position

    August 7, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Re-Extortion at Urology Center: Gov Abba must hear this

    October 10, 2025

    Extortion at Urology Center: Gov Abba must hear this

    October 9, 2025

    Rashin kokarin Kano Pillars da Barau: Sai fa gwamnati ta yi wani abu

    October 7, 2025

    SWAN: Genuine sports stakeholder than NFF, other federation members

    October 6, 2025

    Kungiyar Barau: Kuskuren da Ibrahim Canji, mabiyansa suka tafka

    September 30, 2025
    © 2025 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.