Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Gasar Kofin murnar cika shekara biyun Gwamna Abba: Mai Samba yayi hamdala

      July 28, 2025

      New coach for Pillars this week? Mai Samba confirms

      July 23, 2025

      FISU Games: Prof Yakasai showers admiration on Dikko

      July 18, 2025

      Gobe ne ranar FC Barcelona a Kano

      July 17, 2025

      On-going FISU Games in Germany: NUGA commends Dikko

      July 17, 2025
    • Column

      Ogun State’s Sports Development: My exact dream for Kano’s sports

      July 28, 2025

      Battle of Wits: As Mai Samba, Musa in leadership tussle over Pillars’ soul

      July 21, 2025

      How Governor Yusuf can accelerates sports development in Kano

      July 14, 2025

      TA, players’ recruitment: Why Kano Pillars lagging behind?

      June 30, 2025

      Death of 22 Kano athletes: My condolences to Governor Abba Kabir Yusuf

      June 23, 2025
    • News & Media

      Immortalization of 22 Dead Athletes: Good, but If I were Governor Abba…

      July 7, 2025

      Black Saturday: Stakeholders respond to 22 Kano sportsmen death…recommend strategies to prevent its recurrence

      June 16, 2025

      𝙆𝙎𝙋 starts selling online part-time application forms

      June 4, 2025

      Death of DPO, one other: Thorough investigation underway… as Police urges calm, cooperation

      May 29, 2025

      Rano avoidable carnage: Call for robust Police/Community Relation Committees

      May 29, 2025
    • Analysis

      Power tussle in Pillars: Who is who between  Mai Samba, board and Musa?

      July 16, 2025

      My disappointment with Ahmed Musa’s appointment

      July 9, 2025

      On Team Kano’s low performance at  NSF

      June 3, 2025

      KTSG’s ugly dismissal of Katsina United’s management

      April 16, 2025

      Nigeria’s stadiums safety, security: A matter of urgent attention

      December 1, 2024
    • Personality Profiles

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024

      Dr. Usman Ibrahim Aikawa: New Kano Poly, Director Academic Planning

      January 2, 2024
    Sports Eye
    Home » Hana yan tawagar wasannin nakasassu hakkinsu: A ina aka kwana ne?
    Sports News

    Hana yan tawagar wasannin nakasassu hakkinsu: A ina aka kwana ne?

    Sani YusifBy Sani YusifMarch 18, 2024
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram

    Yau  wata uku cif da zuwa da dawowar yan wasan jihar Kano daga wasan kasa na nakasassu watau (2023 National Para-Games Competition) wanda akayi a Abuja amma har yanzu hukumar wasanni ta jihar Kano (Kano State Sports Commission) bata biya mafi yawancin yan tawagar zuwa Abujan hakkokinsu ba (Daily Travelling Allowances).

    Wani abin haushi datakaici wanda kuma ya zubarwa da hukumar wasannin ta jihar Kano mutunci a idon jamaa shine kasa wani katabus don karbowa mafi yawancin yan tawagar hakkokinsu daga gwamnati kamar yadda suke cewa.

    Bincike ya nuna mummunar wahalar da dukkannin yan tawagar jihar Kano suka sha a lokacin da suke Abuja gabadayansu saboda rashin biyansu alawus din da yakamata a basu tun kamin tafiyar tasu zuwa babban birnin tarayyar Nijeriya, Abuja.

    Idan bamu manta ba, hukumar wasan ta jihar Kano ta tura yan wasa, masu horar dasu, sakatarorin tsare-tsare, likitoci, yan jarida, direbobi, jami’en tsaro da sauransu zuwa Abuja ba tare da basu kudaden alawus dinsu ba (DTA) da alkawarin damka musu kudadensu da sun isa Abuja.

    Amma wani abin takaici da suka isa Abuja sai hukumar wasannin tayi musu kememe al’amarin da ya jefa dukkannin yan tawagar cikin rudani da dimuwa saboda tsanani rashin kudi da suka shiga.

    Wannan ya faru ne saboda mafi yawancinsu basu da kudin cin abinci balantana na inda zasu kwanta ga shi kuma basusan kowa a Abuja ba. Ga kuma rashin kudin sufuri daga can zuwa can.

    Da wuya tayi wuya sai suka koka ta hanyar yan jaridun da suke tare dasu wanda yasa mukaddashin hukumar wassannin ta jihar Kano, Malam Bala Malam magantuwa.

    A jawabinsa ga yan jarida Malam Bala ya bayyana karbar Naira miliyan tara (N9m) cikin miliyan 30 da suka nema daga gwamnati wanda kuma a cewarsa yayi amfani da kudin ya biya kudin rijistar yar wasa al’amarin ya rudarda jama’a da dama.

    A wancen lokacinne Malam Bala yayi alkawarin biyan kowa alawus dinsa da zarar sun komo gida jihar Kano.

    Bincike ya nuna mafiyawancin yan tawagar mutanene masu iyali kuma sun bar gida da alkawarin da sun isa Abuja zasu turowa iyalensu kudin kashewa wanda rashin biyan ya jefasu cikin wata dimuwar.

    Wani  abin haushi kuma shine da suka komo gida alkawarin bai cika ba domin mukaddashin shugaban hukumar yayi biris da maganar, al’amarin da yasa yan tawagar kara magantuwa ta kafafaen yada labarai masu dama.

    Wannance ta firgita shi inda yaje ya samo kudi amma kash a maimakon ya biya dukkannin yan tawagar sai ya zabi wasu a cikinsu har da yan jarida ya biya ya kuma manta da sauran. Al’amarin da jama’a da dama sukayi Allah wadai da kuma kokarin toshe bakin masu magana wanda yayi nasara.

    Wani karin abin takaicin kuma shine cikin mutanen da Malam Bala yaki biya akwai likitoci da dirobobi wadanda arosu akayi daga wasu ma’aikatu don su taimaka a sami nasarar tafiyar.

    Bugu ga kari  su kuma sauran kamarsu sakatarori su suke samo masu horarwa sannan su kuma masu horarwa su samo yan wasa.

    Amma ya biya yan wasa ya manta da sakatarori da masu horarda yan wasan wanda shima babban koma bayane.

    A ganina biyan wasu yan wasa da kuma kin biyan wadancen jami’en ba daidai bane kuma ya nuna rashin sanin aiki da kuma rashin iya gudanarwa.

    A nan nake tunawa Malam Bala yadda ya karbo naira miliyan tara ta farko daga cikin miliyan talatin da gwamnati ta amince a kasha da kuma kudin ya kara  amsowa wadanda bamusan yawansu ba ya biya wasu yan wasa da yan jarida, yakamata ya yi namijin kokari wajen nemo sauran kudaden ya biya masu hakki hakkinsu.

    Yakamata Malam Bala ya sani cewa shi shugabanci ba zama ko iya zama a ofis bane. Yin abin da yakamata a lokacin da yakamata shine shugabanci.

    Yin shiru ba gwaninta bane domin a watan goma sha daya za a sake wani wasan, da wane ido ko fuska zaa kara neman wadannan mutanen don samun gudummawarsu?

    Bugu da kari, shugaban hukumar wassannin yakamata ya  sani cewa da wadannan mutanen da bayaganin kimarsu da mutuncinsu basu agazaba, da tafiyar zuwa Abuja bata yiwu ba

    Tun da har mai girma gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf ya amince a biya banga dalilin da Malam Bala zai rinka baya-baya ba. Ya tashi ya je inda ya kamata don karbowa mutane hakkinsu.

    Ya kuma kamata Malam Bala ya fara amfani da kudaden shiga da hukumarsa take samu daga sitadia ta Sabon Gari da ta Kofar Mata da kuma filin wasa na Ado Bayero Squre don fara rage kudin kafin ya amso wadancan.

    Hakkinsu Hana yan tawagar wasanni
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleJamaa, asa Kano Pillars cikin addua
    Next Article Pain and gain of a writer
    Sani Yusif
    • Website

    I was at the production unit of the Triumph Publishing Company, Kano but my keen interest in sports journalism made me to be sports writer and maintained a sports column called (Sports Eye) after my mentor Sani Muhammad Zaria transferred his service to New Nigeria newspapers in Kaduna. And when the government closed the Triumph in 2012, I was transfered to lectured DTP in the Department of Printing Technology of Kano State Polytechnic. And now that I retired, i used to visit the institution weekends for part-time lecturing.

    Related Posts

    Gasar Kofin murnar cika shekara biyun Gwamna Abba: Mai Samba yayi hamdala

    July 28, 2025

    New coach for Pillars this week? Mai Samba confirms

    July 23, 2025

    FISU Games: Prof Yakasai showers admiration on Dikko

    July 18, 2025

    Gobe ne ranar FC Barcelona a Kano

    July 17, 2025

    On-going FISU Games in Germany: NUGA commends Dikko

    July 17, 2025

    Association of Retired Sports Men and Women debut in Kano

    July 16, 2025
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Gasar Kofin murnar cika shekara biyun Gwamna Abba: Mai Samba yayi hamdala

    July 28, 2025

    Ogun State’s Sports Development: My exact dream for Kano’s sports

    July 28, 2025

    New coach for Pillars this week? Mai Samba confirms

    July 23, 2025

    Battle of Wits: As Mai Samba, Musa in leadership tussle over Pillars’ soul

    July 21, 2025

    FISU Games: Prof Yakasai showers admiration on Dikko

    July 18, 2025
    © 2025 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.