Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

      December 3, 2025

      KMC outshines MAKIA to win 2025 NDLEA Chairman’s Cup

      November 23, 2025

      NFF: Collection of underperforming football administrators

      November 17, 2025

      Northwest Varsity Kano shines at NUGA…wins three medals

      November 15, 2025

      … As Female Basketball Team storms Semi-Finals

      November 15, 2025
    • Column

      AFCON 2025: Whither Nigerian referees?

      December 1, 2025

      If Barau can do it, Pillars too can do it

      November 24, 2025

      Disappointing Outing: Sacking Kano Pillars’ Management, not solution

      November 17, 2025

      My Reflections on Adamu’s Kano Pillars’ poor performance views

      November 10, 2025

      Fitness Test: Over 1,500 Referees, Assessors to converge in Kano ‘morrow

      November 7, 2025
    • News & Media

      2025 CIPPON Annual General Meeting (AGM) to Hold in Kano

      November 22, 2025

      Congregation Election: ADUSTECH’s NASU, SSANU candidates triumph

      November 18, 2025

      Retirement: Dantiye congratulates Yakasai

      November 14, 2025

      70th Birthday: Dr. Muhammad Felicitates with Sen. Ibrahim Shekarau

      November 5, 2025

      70th Birthday: Dr. Muhammad Felicitates with Sen. Shekarau

      November 5, 2025
    • Analysis

      Wa ke son ganin bayan su Ali Nayara Mai Samba?

      December 1, 2025

      Now that Pillars has at last broken long-standing jinx…

      November 26, 2025

      To escape relegation: Pillars urged to defeat Ikorodu City

      November 23, 2025

      Kano Pillars FC: Ta yaya muka sami kanmu a haka?

      November 21, 2025

      Jama’a, a ina muka samo ko koyo wannan kuma?

      November 20, 2025
    • Personality Profiles

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024

      Dr. Usman Ibrahim Aikawa: New Kano Poly, Director Academic Planning

      January 2, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Kungiyar Barau: Kuskuren da Ibrahim Canji, mabiyansa suka tafka
    Sports News

    Kungiyar Barau: Kuskuren da Ibrahim Canji, mabiyansa suka tafka

    Sani YusifBy Sani YusifSeptember 30, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    1b

    Ana wata ga wata, domin a daidai lokacin da kungiyar kwallon kafa ta Barau ta bankado wasu almindahanonin kudi masu nauyi da ake ta tafkawa a kungiyar wanda kuma ake zargin shugabancin Ibrahim Shitu Canji yakeyi, sai gashi Ibrahim Canji na nuna wasu halaye ga kungiyar wadanda basu kamata ba ko kadan.

    Wata majiya mai tushi ta shedawa wannan kafa cewa tun lokacin da aka bankado almindahanonin zabtarewa yan wasan kungiyar Barau kusan rabin albashinsu yasa mamallakin kungiyar, Sanata Barau Jibrin Maliya ya umarci da gabatar da canje-canje a tsarin shugabancin kungiyar.

    Yin binciken ke da wuya aka bankado wani abu mara dadinji, watau yadda ake zabtarewa wasu daga cikin yan wasan kungiyar Barau din rabin albashinsu ba gaira ba dalilin kuma babu dalilin yin hakan.

    Haka kuma rashin samun nasarar kungiyar ta Barau a wasannin da ta buga guda hudu duk da makudankudin da ake kashewa kungiyan ya bayyana rashin kwarewa da gogewar shugabancin Ibrahim Shitu Canji a harkar wanda shima ya taimaka wajen samarda canje-canjen a kungiyar Barau din.

    Hakika canje-canjen  wanda ya kawo wasu mutum biyu masu kwarewa da ilmin abin ya ragewa shi Ibrahim Shitu Canji karfin fada a ji a kungiyar sosai, abinda ake ganin shi ya hasala shi.

    Shi wannan canje-canjen ya shigo da tsohon shugaban kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, Alhaji Kabiru Baita, a matsayin maitaimakin shugaba da kuma Dominik Yofa, tsohon shugaban kungiyar kwallon kafa ta Lobi dake jihar Binuwe, a matsayin babban manajan kungiyar kwallon kafa ta Barau.

    Ko shakka babu wata majiya ta tabbatarwa wannan kafa cewa wannan al’amarin baiyiwa Ibrahim Canji dadi ba domin a da shine ke da wuka kuma shine da nama domin Sanata Barau ya bar masa komai a hannunsa.

    Amma kash, a maimakon shugabancin Ibrahim Canji yayi abinda yakamata, sai a wata majiya suka kawo son zuciya wanda baiyiwa shi Sanata Barau da kungiyar dadi ba wanda ya jawo samarda wani tsari da zai shigo da wasu don daidaita al’amarin.

    Hakika shigowar wannan mutum biyun watau Baita da Dominik cikin tsarin shugabancin kungiyar baiyiwa Ibrahim Canji dadi ba domin ya rage masa kafin fada aji a cikin kungiyar da yake tunkaho shine ruhinta a jihar Kano.

    Wani bincike ya nuna cewa tun shigowa da kuma kama aikin wadanda mutum biyun, watau Kabiru Baita da kuma Dominik Yofa, Ibrahin Canji ya canja salo da kuma ta yin guna guni da kuma nuna halin ni ‘yasu.

    Fara nuna halaye marasa kyau da Ibrahim Canji yakeyi a harkokin kungiyar sai fitowa fili sukeyi kullum, domin ko tafiya zuwa wasan kungiyar da tayi da kungiyar Kun Khalifa bai jeba kuma baaga keyarsa a wajen haduwa don tafiya wasan ba.

    Wata majiyar ta tabbatarwa wannan kafa cewa kafin tafiyar kungiyar Barau zuwa wancen wasannata da kungiyar Kun Khalifa, an jira kuma, an kuma nemi shi Ibrahim Canji amma ba’aganshi ba kuma ba’aji daga gareshiba.

    Kuma a lokacin da aka nemeshi ta lambobin wayoyinsa shima baayi nasarar saminshiba domin dukkanninsu a rufe suke.

    Haka aka hakura aka tafi filin jirgin sama na Malam Aminu Kano don shiga jirgin sama aka kuma tafi kuma aka sami nasara ba Ibrahim Shitu Canji ba mukarrabensa. Wannan ba karamin kuskure bane domin ita maganar almindahana bafa fito da ita akayi ba har izuwa wnnan lokacin abin a cikin zargi yake.

    Bincike ya nuna cewa dukkannin makarraben Ibrahim Canji dake rike da wani mikami a kungiyar kamarsu Yahaya Muhammad, daraktan wasannin kungiyar, Jabir Hassan, Technical Consultant, Abubakar Sadiq, mai kula da bangaren kasuwancin kungiyar, Umar Lawan wanda shine sakatare da kuma Isma’il Mahmoud, mai kula da walwala da jin dadin kungiyar sun juyawa kungiyar baya domin nuna biyayyarsu ga Ibrahim Canji saboda kin bin kungiyar zuwa wasanta da Kun Khalifa.

    Hakika rashin zuwansu Ibrahim Canji da mukarrabensa baiyi wani tasiri ba domin a maimakon samun rashin nasara, kungiyar Barau samun nasararta ta farko tayi a kan masu masaukinsu.

    Sai dai wata kafa ta bayyana mana cewa wannan rashin kyautawa da Canji da mukarrabensa sukayi bazai musu dadi ba domin kungiyar na iya tunanin ladaftar dasu.

    Wannan kafa tana kira ga Ibrahim Canji da ya mukarrabensa da su canja tunani domin ita rayuwa juyawa takeyi. Ko da baa samesu laifin komi ba, bawanda zaita kasha kudinsa akan kungiya wadda ba nasara kuma ya tsaya yana kallo. Dole yayi wani abu ko hobbasa da zai kawo gyara.

    A ganinmu Ibrahim Canji da mukarrabensa godewa Allah da kuma mai kungiyar yakamata suyi ba tawaye ba, domin laifin da ake zarginsu babbane kuma tunda bai fallasa ba, sai suyi shiru kuma su gyara ba yin tawaye ba.

    Su sani fa, anayi da kai…

    Canji da Ibrahim kungiyar Barau Kuskuren ya tafka
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleChanges in Barau FC: Where DSP Barau Jibrin fumbles
    Next Article SWAN: Genuine sports stakeholder than NFF, other federation members
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

    December 3, 2025

    KMC outshines MAKIA to win 2025 NDLEA Chairman’s Cup

    November 23, 2025

    NFF: Collection of underperforming football administrators

    November 17, 2025

    Northwest Varsity Kano shines at NUGA…wins three medals

    November 15, 2025

    … As Female Basketball Team storms Semi-Finals

    November 15, 2025

    NUGA: BUK makes history following first–ever Volleyball Gold thrilling Final

    November 15, 2025
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

    December 3, 2025

    Wa ke son ganin bayan su Ali Nayara Mai Samba?

    December 1, 2025

    AFCON 2025: Whither Nigerian referees?

    December 1, 2025

    Now that Pillars has at last broken long-standing jinx…

    November 26, 2025

    If Barau can do it, Pillars too can do it

    November 24, 2025
    © 2025 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.