Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

      July 14, 2026

      New Kano Pillars Management: Any hope for real change?

      July 13, 2026

      Gombe Emir’s Cup: Organisers unveil quarter-final fixtures, match dates

      July 10, 2026

      Gombe Emir’s Cup Quarter-Finals set as Eight Clubs progress

      July 8, 2026

      Babangida takes helm of Kano State Sports Commission

      July 6, 2026
    • Column

      Has Barau FC management lost sight of Senator Barau’s vision?

      July 24, 2026

      Free transfer blow: Should Kano Pillars have let Fabian Nworie leave for nothing?

      July 17, 2026

      With full government support, Babangida, Maizare, others must produce results

      July 10, 2026

      Gov. Abba’s listening approach: Key to reviving Kano Pillars, Kano Sports Commission

      July 3, 2026

      Kano State Sports under siege: Governor Abba must hear it

      June 26, 2026
    • News & Media

      Keyamo, Musawa confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

      July 24, 2026

      Keyamo, Musawa Confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

      July 24, 2026

      Katsina Government seeks Kano’s expertise to establish Culture, Reorientation Agency

      July 15, 2026

      NTDA partners Ringo Sport Club for NISPRISPORT 2026

      July 15, 2026

      NASTOCE 2026: Chief Abiodun Odusanwo, Dr. Badaki Aliyu Earn Meritorious Honours

      July 14, 2026
    • Analysis

      Kano Sports: Huge expectations for new Kano Pillars, Sports Commission Boards

      June 29, 2026

      Kano Pillars’ survival hopes alive despite tough battle ahead

      May 22, 2026

      NPFL survival at stake: Relegation battle heads into final day

      May 14, 2026

      Kano Pillars: Final words before crucial Plateau United FC encounter

      May 12, 2026

      Alleged Bias in Kano Sports Support: What Kano FA Should Address

      May 5, 2026
    • Personality Profiles

      Engr. Aikawa assumes Office as pioneer Deputy Rector (Academics)

      July 6, 2026

      Making of a Leader: Dr. Garba A. Adamu’s journey from laboratory to leadership

      July 4, 2026

      AbdulGaffar I. Dawakin Tofa: Shaping public discourse through journalism, broadcasting

      June 24, 2026

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Anya ba hakkin yan wasa da ma su horaswa ke bin Pillars, Barau ba?
    Sports News

    Anya ba hakkin yan wasa da ma su horaswa ke bin Pillars, Barau ba?

    Sani YusifBy Sani YusifNovember 6, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    1b

    “Anya kuwa ba alhakin wasu yan wasa da masu horar da yan wasan ke bin kungiyoyin Kano Pillars da Barau dake cikin gasar pirimiya ta kasa watau NPFL ke bin suba?”

    Wannan tambayar kuma mai wuyar amsawa ta biyo baya ne saboda ganin yadda kungiyoyin biyu watau Pillars da Barau suka kasa tabika wani abin azo a gani tun farko kakar wasa ta bana zuwa wannan lokacin.

    Duk da kowa yasan cewa da kungiyar Kano Pillars da ta Barau din babu mai wata matsalar kudi ko kayan aiki, amma sun kasa komai a wannan kakar wasan ta bana. Duk da suna taka waSa iya gwargwado ko karfinsu.

    Domin kwana kwanannan gwamnatin jihar Kano ta gwangwaje kungiyar Kano Pillars da sabbabbin motoci don sawwake musu wahalar tafiye tafiyen zuwa wasansu na waje.

    Ita kuma kungiyar Barau a jirgin sama suke kai yan wasansu zuwa wasansu na waje don rage ko kawar musu da gajiyar dogowar tafiya mai nisa.

    Bincike ya nuna cewa yan wasa da yawa da kuma masu horaswa (coaches) na dukkanin kungiyoyin biyu watau Pillars da Barau nada wani hakki a tare da kungiyoyin biyu wanda shine ke bin kungiyoyin.

    Wannan ta sa aka fara danganta rashin nasara ko tabika wani abin azo a gani na kungiyoyin biyu a gasar pirimiya wadda wannan makon take shiga makonta na goma.

    Binciken ya kuma nuna cewa cin zarafi da kungiyoyin biyu suka yiwa masu horasda yan wasansu (coaches) a baya ba zai barsu suyi wani abin kirki a gasar ba.

    A bangaren Kano Pillars anga yadda mahukuntan kungiyar tare da hadinkan wasu magoyabaya kungiyar suka sa masu horaswa biyu kamar Audu Maikaba da Usman Abdallah a gaba wanda har saida akaga bayansu.

    Bincike ya sake nuna yadda masu horaswar biyu suka bar kungiyar ba dan suna so ba, saidai dan babu yadda za suyi.

    A bangaren yan wasa kuwa, akwai labarin fifita wasu yan wasan akan wasu saboda kawai su yaran wani ko wasu daga cikin shugabannin kungiyarne.

    Akwai rade-radin cewa idan dan wasa bashi da tagomashin wani ko wasu daga cikin shugabannin Kano Pillars ko magoyabayansu to sam bazai kai labara ba duk kyau ko kokarinsa.

    Koshima mai horaswa da kungiyar Kano Pillars ta kora baya-bayannan watau Evans Ogenyi mutane da dama suna ganin baa kyauta masa ba domin baa bashi damar kare kansa ba.

    A bangaren kungiyar Barau kuwa, kowa yaga yadda Rabiu Tata yayi kokari ba dare ba rana yakai kungiyar matakin da take akai yau, amma meya faru? Sai kawai aka kakaba masa wani daga sama wai a sunnan babban mai horaswa.

    Ha kuma bincike ya nuna cewa yawancin yan wasan da suka sha wahalar kai kungiyar Barau matakinta na yanzu, abin haushi anyi watsi dasu kuma babu wani tagomashi da akayi musu don nuna godiya da kokarinsu.

    A bangaren Barau dindai, akwai zargin cinzalin yan wasa da yawa wanda su kadai baza su bar kungiyar Barau din taka wata rawar kirki ba.

    Zargi na farko wanda ake ganin alhakinsa zai iya nisanta kungiyar Barau daga nasara shine wanda aka salami yan wasa ba tare da gode musu da kuma basu hakkokinsuba.

    Zargi na biyu shine hana wasu yan wasan kyautar Babura daya-daya da Sanata Barau Jibrin Maliya ya basu bayan samun nasarar kai kungiyar gasar pirimiya ta kasa.

    Wannan ta faru ne domin wasu ba a basu baburar kamar yadda shi sanata Barau yace a bada ba. Ance wasu an basu amma wasu mutum biyu-biyu ko sama da haka aka hada aka bawa.

    Haka kuma ana zargin yiwa yan wasan kungiyar Barau gaftare da gibin albashinsu  ko kuma wata kyautar kudi da Sanata Barau ya bada don a rabawa yan wasan kungiyar wanda yakamata sanata yasa abincika.

    Wadannan da wasu zarge-zargen sune wasu daga cikin ahakin yan wasa dana cin zarafin masu horaswa wanda ke bin kungiyoyin Kano Pillars dana Barau .

    A ganina yakamata baa makaraab, a duba idan an tabbatar to akirawosu a basu hakuri don kungiyoyin biyu su cigaba da samun tagomashi.

    Anya ba hakkin kuwa yan wasa
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous Article70th Birthday: Dr. Muhammad Felicitates with Sen. Ibrahim Shekarau
    Next Article Fitness Test: Over 1,500 Referees, Assessors to converge in Kano ‘morrow
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

    July 14, 2026

    New Kano Pillars Management: Any hope for real change?

    July 13, 2026

    Gombe Emir’s Cup: Organisers unveil quarter-final fixtures, match dates

    July 10, 2026

    Gombe Emir’s Cup Quarter-Finals set as Eight Clubs progress

    July 8, 2026

    Babangida takes helm of Kano State Sports Commission

    July 6, 2026

    Sports sector reforms: National Sports Commission earns ABU’s praise

    July 6, 2026
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Keyamo, Musawa confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

    July 24, 2026

    Keyamo, Musawa Confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

    July 24, 2026

    Has Barau FC management lost sight of Senator Barau’s vision?

    July 24, 2026

    Free transfer blow: Should Kano Pillars have let Fabian Nworie leave for nothing?

    July 17, 2026

    Katsina Government seeks Kano’s expertise to establish Culture, Reorientation Agency

    July 15, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.