Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

      December 3, 2025

      KMC outshines MAKIA to win 2025 NDLEA Chairman’s Cup

      November 23, 2025

      NFF: Collection of underperforming football administrators

      November 17, 2025

      Northwest Varsity Kano shines at NUGA…wins three medals

      November 15, 2025

      … As Female Basketball Team storms Semi-Finals

      November 15, 2025
    • Column

      Sports development in Kano: Expert’s advice

      December 8, 2025

      AFCON 2025: Whither Nigerian referees?

      December 1, 2025

      If Barau can do it, Pillars too can do it

      November 24, 2025

      Disappointing Outing: Sacking Kano Pillars’ Management, not solution

      November 17, 2025

      My Reflections on Adamu’s Kano Pillars’ poor performance views

      November 10, 2025
    • News & Media

      Oseni replaces Ramat as NERC chairman after Senate rejection

      December 19, 2025

      Ahned Musa: Honoring 15 Years of Dedication and Selfless Service

      December 17, 2025

      2025 CIPPON Annual General Meeting (AGM) to Hold in Kano

      November 22, 2025

      Congregation Election: ADUSTECH’s NASU, SSANU candidates triumph

      November 18, 2025

      Retirement: Dantiye congratulates Yakasai

      November 14, 2025
    • Analysis

      My Sports Agenda for North-West Development Commission

      December 15, 2025

      Multiple birth dates issues: Where Gombe’s call went off track

      December 11, 2025

      2025 Premier Handball League: Why is Kano absent?

      December 5, 2025

      Wa ke son ganin bayan su Ali Nayara Mai Samba?

      December 1, 2025

      Now that Pillars has at last broken long-standing jinx…

      November 26, 2025
    • Personality Profiles

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Anya ba hakkin yan wasa da ma su horaswa ke bin Pillars, Barau ba?
    Sports News

    Anya ba hakkin yan wasa da ma su horaswa ke bin Pillars, Barau ba?

    Sani YusifBy Sani YusifNovember 6, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    1b

    “Anya kuwa ba alhakin wasu yan wasa da masu horar da yan wasan ke bin kungiyoyin Kano Pillars da Barau dake cikin gasar pirimiya ta kasa watau NPFL ke bin suba?”

    Wannan tambayar kuma mai wuyar amsawa ta biyo baya ne saboda ganin yadda kungiyoyin biyu watau Pillars da Barau suka kasa tabika wani abin azo a gani tun farko kakar wasa ta bana zuwa wannan lokacin.

    Duk da kowa yasan cewa da kungiyar Kano Pillars da ta Barau din babu mai wata matsalar kudi ko kayan aiki, amma sun kasa komai a wannan kakar wasan ta bana. Duk da suna taka waSa iya gwargwado ko karfinsu.

    Domin kwana kwanannan gwamnatin jihar Kano ta gwangwaje kungiyar Kano Pillars da sabbabbin motoci don sawwake musu wahalar tafiye tafiyen zuwa wasansu na waje.

    Ita kuma kungiyar Barau a jirgin sama suke kai yan wasansu zuwa wasansu na waje don rage ko kawar musu da gajiyar dogowar tafiya mai nisa.

    Bincike ya nuna cewa yan wasa da yawa da kuma masu horaswa (coaches) na dukkanin kungiyoyin biyu watau Pillars da Barau nada wani hakki a tare da kungiyoyin biyu wanda shine ke bin kungiyoyin.

    Wannan ta sa aka fara danganta rashin nasara ko tabika wani abin azo a gani na kungiyoyin biyu a gasar pirimiya wadda wannan makon take shiga makonta na goma.

    Binciken ya kuma nuna cewa cin zarafi da kungiyoyin biyu suka yiwa masu horasda yan wasansu (coaches) a baya ba zai barsu suyi wani abin kirki a gasar ba.

    A bangaren Kano Pillars anga yadda mahukuntan kungiyar tare da hadinkan wasu magoyabaya kungiyar suka sa masu horaswa biyu kamar Audu Maikaba da Usman Abdallah a gaba wanda har saida akaga bayansu.

    Bincike ya sake nuna yadda masu horaswar biyu suka bar kungiyar ba dan suna so ba, saidai dan babu yadda za suyi.

    A bangaren yan wasa kuwa, akwai labarin fifita wasu yan wasan akan wasu saboda kawai su yaran wani ko wasu daga cikin shugabannin kungiyarne.

    Akwai rade-radin cewa idan dan wasa bashi da tagomashin wani ko wasu daga cikin shugabannin Kano Pillars ko magoyabayansu to sam bazai kai labara ba duk kyau ko kokarinsa.

    Koshima mai horaswa da kungiyar Kano Pillars ta kora baya-bayannan watau Evans Ogenyi mutane da dama suna ganin baa kyauta masa ba domin baa bashi damar kare kansa ba.

    A bangaren kungiyar Barau kuwa, kowa yaga yadda Rabiu Tata yayi kokari ba dare ba rana yakai kungiyar matakin da take akai yau, amma meya faru? Sai kawai aka kakaba masa wani daga sama wai a sunnan babban mai horaswa.

    Ha kuma bincike ya nuna cewa yawancin yan wasan da suka sha wahalar kai kungiyar Barau matakinta na yanzu, abin haushi anyi watsi dasu kuma babu wani tagomashi da akayi musu don nuna godiya da kokarinsu.

    A bangaren Barau dindai, akwai zargin cinzalin yan wasa da yawa wanda su kadai baza su bar kungiyar Barau din taka wata rawar kirki ba.

    Zargi na farko wanda ake ganin alhakinsa zai iya nisanta kungiyar Barau daga nasara shine wanda aka salami yan wasa ba tare da gode musu da kuma basu hakkokinsuba.

    Zargi na biyu shine hana wasu yan wasan kyautar Babura daya-daya da Sanata Barau Jibrin Maliya ya basu bayan samun nasarar kai kungiyar gasar pirimiya ta kasa.

    Wannan ta faru ne domin wasu ba a basu baburar kamar yadda shi sanata Barau yace a bada ba. Ance wasu an basu amma wasu mutum biyu-biyu ko sama da haka aka hada aka bawa.

    Haka kuma ana zargin yiwa yan wasan kungiyar Barau gaftare da gibin albashinsu  ko kuma wata kyautar kudi da Sanata Barau ya bada don a rabawa yan wasan kungiyar wanda yakamata sanata yasa abincika.

    Wadannan da wasu zarge-zargen sune wasu daga cikin ahakin yan wasa dana cin zarafin masu horaswa wanda ke bin kungiyoyin Kano Pillars dana Barau .

    A ganina yakamata baa makaraab, a duba idan an tabbatar to akirawosu a basu hakuri don kungiyoyin biyu su cigaba da samun tagomashi.

    Anya ba hakkin kuwa yan wasa
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous Article70th Birthday: Dr. Muhammad Felicitates with Sen. Ibrahim Shekarau
    Next Article Fitness Test: Over 1,500 Referees, Assessors to converge in Kano ‘morrow
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

    December 3, 2025

    KMC outshines MAKIA to win 2025 NDLEA Chairman’s Cup

    November 23, 2025

    NFF: Collection of underperforming football administrators

    November 17, 2025

    Northwest Varsity Kano shines at NUGA…wins three medals

    November 15, 2025

    … As Female Basketball Team storms Semi-Finals

    November 15, 2025

    NUGA: BUK makes history following first–ever Volleyball Gold thrilling Final

    November 15, 2025
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Oseni replaces Ramat as NERC chairman after Senate rejection

    December 19, 2025

    Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

    December 19, 2025

    Ahned Musa: Honoring 15 Years of Dedication and Selfless Service

    December 17, 2025

    My Sports Agenda for North-West Development Commission

    December 15, 2025

    Multiple birth dates issues: Where Gombe’s call went off track

    December 11, 2025
    © 2025 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.