Dare warsa gadon mulkin karamar hukumar Fagge keda wuya, sabon shugaban karamar hukumar Fagge, Hon. Salisu Masu ya bayyana rushe dukkannin sassuna sama da 40 da ake karbar kudin shigar karamar hukumar baki dayansu.

Ayyana rushe masu karbar kudin shigar na karamar hukumar, sai komi ya tsaya cak inda shigar kudi aljihun karamar hukumar ya tsaya  shima cak.

Bincike ya nuna cewa dakatar da masu karbar kudin shigar karamar hukumar yin aikinsu yasa karamar hukumar asarar miliyoyin nairori.

Mutane da yawa da muka zanta dasu sun nuna mamakin yin hakan domin daga lokacin da shugaba Masu ya ayyana dakatarwar zuwa yau kusan wata guda kenan, kuma yakamata ace duk abinada zai kawo tsaikon sake sababbin masu tattara kudin shiga a kauce masa.

Wata majiyar ta nuna cewa tsaikon nada sababbin masu tattara kudin shigar ya samune saboda matsin lamba da wasu keyi akan aba damar tattara kudin da kuma inda suke so a tura su.

Wata majiyar kuma ta nuna shaawar wasu manyan jigajigen siyasar Fagge game da tattara kudin shigar don samawa mabiyansu madafa.

Koma me ake ciki yakamata shugabannin karamar hukumar su farka domin dakatar da sulalewar ko asarar miliyoyin kudin shiga.

By Sani Yusif

I was at the production unit of the Triumph Publishing Company, Kano but my keen interest in sports journalism made me to be sports writer and maintained a sports column called (Sports Eye) after my mentor Sani Muhammad Zaria transferred his service to New Nigeria newspapers in Kaduna. And when the government closed the Triumph in 2012, I was transfered to lectured DTP in the Department of Printing Technology of Kano State Polytechnic. And now that I retired, i used to visit the institution weekends for part-time lecturing.