Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Nigeria’s Sports Tourism takes center stage …as NASTOCE 2026 launches in Abuja

      February 8, 2026

      Kano’s Gwadabe, four others for FIFA’s course in Kigali

      February 5, 2026

      Barau FC breaks new ground with Pre-Kick-off bonus payment

      February 4, 2026

      Adamu clinches landslide victory as Lady Captain of TYB Golf Club

      February 1, 2026

      Novelty football match: Kurmawa inmates overpower NDLEA’s Marwa’s Boys

      January 29, 2026
    • Column

      NPFL Under Fire: Governance, sanctions with fight for transparency

      February 9, 2026

      Sportyseye in prison: Lifetime experience of agony and joy

      February 2, 2026

      Amidst friends, family, others: Chairman Gwadabe’s daughter Ameera weds

      January 26, 2026

      In defence of BUA’s Super Eagles largess

      January 19, 2026

      Changes needed in Kano State Sports Commission

      January 12, 2026
    • News & Media

      Kano Football Coaches host Modern Coaching Seminar for members

      January 7, 2026

      Oseni replaces Ramat as NERC chairman after Senate rejection

      December 19, 2025

      Ahned Musa: Honoring 15 Years of Dedication and Selfless Service

      December 17, 2025

      2025 CIPPON Annual General Meeting (AGM) to Hold in Kano

      November 22, 2025

      Congregation Election: ADUSTECH’s NASU, SSANU candidates triumph

      November 18, 2025
    • Analysis

      Memo to KNSG’s committee on Kano Pillars’ performance

      February 9, 2026

      Re-Calls on Gov. Yusuf to Dissolve Kano Pillars Board, but retain GM Musa

      February 6, 2026

      Kano Pillars and Sports Commission: Story of Dwindling Fortunes

      February 5, 2026

      Jan kafar Pillars wajen ɗaukar sababbin ’yan wasa: Me ke faruwa?

      February 4, 2026

      Gaskiyar banbanci tsakanin Kano Pillars da Barau FC

      February 4, 2026
    • Personality Profiles

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Kicibis da Mai  Samba: Abubuwan da na fada masa
    Sports News

    Kicibis da Mai  Samba: Abubuwan da na fada masa

    Sani YusifBy Sani YusifAugust 19, 2024
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram

    Kwanaki kadan da suka wuce  da rana tsaka, nayi kicibis da Ali Nayara Mai Samba, sabon shugaban hukumar gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars.

    Hakan ta faru ne ina zaune da wusu mutane a kofar gidana dake Kurna Asabe muna tattauna lamarin rayuwa.

    Kwatsam sai naji sallama ta gefen hagu na. Amma kafin na juya naga mai yin sallama sai na amsa kuma sannan na juya don naga mai yin sallamar.

    Duba me yimin sallama keda wuya sai naga ashe Alhaji Ali Nayara Mai Samba tare da wani dan makwabcina wanda ake kira Baban Hajiya suka kawomin ziyara don mu gaisa.

    Nan take na tashi na tarbeshi na kuma mika masa hannu amma dukkanninsu suka nuke suka ki yin misabahar dani don girmamawa.

    Bayan mun gaisa sai nayi masa murnar samun matsayin shugabancin hukumar gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, na kuma masa adduar fatan alheri, nasara da kuma gamawa lafiya.

    Da Ali Mai Samba ya bude bakinsa sai nima ya godemin kuma ya nemine dana cigaba da bashi shawarwari don yin nasara da kuma cigaban kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars.

    Kafin ya juya ya tafi sai na nuna masa kalu balen dake gabansa da kuma yadda yakamata yayi don yakai labara.

    Abu na farko dana fada masa shine ya dage ya zauna da yan kwamitinsa goma sha uku lafiya. Yayi amfani da darrasan da ya koya wajen rusasshen shugabancin hukumar baya wanda shima daya daga cikinsu ne.

    Ka da ya sake ya dauki matsayinsa na shugaba yafi kowa a cikinsu. A’a ya daukesu abokan aiki domin tare aka nadasu kuma tare za suyi aiki na gudanarwa da kuma cigaban Kano Pillars.

    Na fada masa ya rinka kiran yan kwamitinsa taro a duk lokacin da wata matsala ta taso don jin abinda ke bakinsu. Kuma kada ya rinka daukar mataki ko matsaya kai tsaye ba tare da jin ta bakinsu ba.

    Na kuma bashi shawarar kafa kwamitin kwararru ((Technical Committee) don yin aiki tareda masu horar da yan was an kungiyar.

    Anan ne  nace masa zai iya zabo masana wadanda suka kware ya hada da wasu daga cikin yan kwamitinsa don kasancewa yan kwamitin kwararrun.

    Na uku na fada masa cewa ya lura da yadda ake daukar yan wasa a Kano Pillars kuma ya kawo masalaha wadda zata taimakawa Kano Pillars kuma ta taimakawa gwamnati.

    Ta daukar yan wasa nata na kanta kawai kungiyar Kano Pillars zata iya rike kanta kuma ta samawa gwamnati manyan kudade a matsayin kudin shiga a duk lokacin  da zata sayarda dan wasanta ga wata kungiya ko gida ko waje.   

    Na bawa Mai Samba shawarar dakatar da daukar danwasa ko yan wasa na zango daya daga (Agent(s)). Domin ana cutar kungiyar da kuma gwamnati sosai ta wannan bigiren. Na bashi shawarar daukan dan wasa ko yan wasa shekara biyu ko uku.

    Domin ta hakane kawai kungiyar da kuma gwamnatin jihar Kano zasu amfana da kudi masu yawa a duk lokacin da wani dan wasan zai canja sheka zuwa wata kungiyar.

    Na kuma  bashi shawarar zama lafiya da kungiyar magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars. Na fada mahimmancinsu da kuma yi masa nasihar mutuntasu da kuma  daukarsu abokan aiki.

    Ya daukesu abokan aiki kuma ya rinka tuntubarsu lokaci-lokaci don sanin matsalolinsu da kuma taimaka musu sharesu.

     Na nuna masa  amfani da kuma tasirinsu musamman wajen bada goyon bayan da ake so a duk lokacin da Kano Pillars ke wasa gida ko waje.

    Game da mutanenmu yan jarida kuwa na fadawa Mai Samba da suma ya kula dasu da muradunsu. Kada ya bare ya samu matsala dasu.

    Na masa murnar samun mutum biyu a cikin kwamitinsa wadanda aka cemin dukkanninsu kwararrun yan jaridane da kuma bashi shawarar saurararsu don samun daidaito da abokan aikinsu.

    Sai na sake  masa fatan alheri ya juya suka tafi.

    Kicibis
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleNigeria’s poor Paris outing: Minister’s apology not enough
    Next Article Rantsuwar sababbin shugabannin kungiyar Yankasuwar Babban Layi
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Nigeria’s Sports Tourism takes center stage …as NASTOCE 2026 launches in Abuja

    February 8, 2026

    Kano’s Gwadabe, four others for FIFA’s course in Kigali

    February 5, 2026

    Barau FC breaks new ground with Pre-Kick-off bonus payment

    February 4, 2026

    Adamu clinches landslide victory as Lady Captain of TYB Golf Club

    February 1, 2026

    Novelty football match: Kurmawa inmates overpower NDLEA’s Marwa’s Boys

    January 29, 2026

    NUGA Games: UniCalabar set to host 28th edition

    January 21, 2026
    View 1 Comment

    1 Comment

    1. Zahraddeen zakari on August 19, 2024 12:22 pm

      Masha Allah, Allah ya kara taimako

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Memo to KNSG’s committee on Kano Pillars’ performance

    February 9, 2026

    NPFL Under Fire: Governance, sanctions with fight for transparency

    February 9, 2026

    Nigeria’s Sports Tourism takes center stage …as NASTOCE 2026 launches in Abuja

    February 8, 2026

    Re-Calls on Gov. Yusuf to Dissolve Kano Pillars Board, but retain GM Musa

    February 6, 2026

    Kano’s Gwadabe, four others for FIFA’s course in Kigali

    February 5, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.