Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

      July 14, 2026

      New Kano Pillars Management: Any hope for real change?

      July 13, 2026

      Gombe Emir’s Cup: Organisers unveil quarter-final fixtures, match dates

      July 10, 2026

      Gombe Emir’s Cup Quarter-Finals set as Eight Clubs progress

      July 8, 2026

      Babangida takes helm of Kano State Sports Commission

      July 6, 2026
    • Column

      Free transfer blow: Should Kano Pillars have let Fabian Nworie leave for nothing?

      July 17, 2026

      With full government support, Babangida, Maizare, others must produce results

      July 10, 2026

      Gov. Abba’s listening approach: Key to reviving Kano Pillars, Kano Sports Commission

      July 3, 2026

      Kano State Sports under siege: Governor Abba must hear it

      June 26, 2026

      Madrid, Barcelona Supporters’ friendly meeting in Kano: A welcome initiative, but…

      June 19, 2026
    • News & Media

      Katsina Government seeks Kano’s expertise to establish Culture, Reorientation Agency

      July 15, 2026

      NTDA partners Ringo Sport Club for NISPRISPORT 2026

      July 15, 2026

      NASTOCE 2026: Chief Abiodun Odusanwo, Dr. Badaki Aliyu Earn Meritorious Honours

      July 14, 2026

      To Reposition Broadcasting in Nigeria: BON constitutes Six Strategic Committees

      July 8, 2026

      Not only NSC, EFCC should investigates NFF, other federations too

      June 5, 2026
    • Analysis

      Kano Sports: Huge expectations for new Kano Pillars, Sports Commission Boards

      June 29, 2026

      Kano Pillars’ survival hopes alive despite tough battle ahead

      May 22, 2026

      NPFL survival at stake: Relegation battle heads into final day

      May 14, 2026

      Kano Pillars: Final words before crucial Plateau United FC encounter

      May 12, 2026

      Alleged Bias in Kano Sports Support: What Kano FA Should Address

      May 5, 2026
    • Personality Profiles

      Engr. Aikawa assumes Office as pioneer Deputy Rector (Academics)

      July 6, 2026

      Making of a Leader: Dr. Garba A. Adamu’s journey from laboratory to leadership

      July 4, 2026

      AbdulGaffar I. Dawakin Tofa: Shaping public discourse through journalism, broadcasting

      June 24, 2026

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Kicibis da Mai  Samba: Abubuwan da na fada masa
    Sports News

    Kicibis da Mai  Samba: Abubuwan da na fada masa

    Sani YusifBy Sani YusifAugust 19, 2024
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram

    Kwanaki kadan da suka wuce  da rana tsaka, nayi kicibis da Ali Nayara Mai Samba, sabon shugaban hukumar gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars.

    Hakan ta faru ne ina zaune da wusu mutane a kofar gidana dake Kurna Asabe muna tattauna lamarin rayuwa.

    Kwatsam sai naji sallama ta gefen hagu na. Amma kafin na juya naga mai yin sallama sai na amsa kuma sannan na juya don naga mai yin sallamar.

    Duba me yimin sallama keda wuya sai naga ashe Alhaji Ali Nayara Mai Samba tare da wani dan makwabcina wanda ake kira Baban Hajiya suka kawomin ziyara don mu gaisa.

    Nan take na tashi na tarbeshi na kuma mika masa hannu amma dukkanninsu suka nuke suka ki yin misabahar dani don girmamawa.

    Bayan mun gaisa sai nayi masa murnar samun matsayin shugabancin hukumar gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, na kuma masa adduar fatan alheri, nasara da kuma gamawa lafiya.

    Da Ali Mai Samba ya bude bakinsa sai nima ya godemin kuma ya nemine dana cigaba da bashi shawarwari don yin nasara da kuma cigaban kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars.

    Kafin ya juya ya tafi sai na nuna masa kalu balen dake gabansa da kuma yadda yakamata yayi don yakai labara.

    Abu na farko dana fada masa shine ya dage ya zauna da yan kwamitinsa goma sha uku lafiya. Yayi amfani da darrasan da ya koya wajen rusasshen shugabancin hukumar baya wanda shima daya daga cikinsu ne.

    Ka da ya sake ya dauki matsayinsa na shugaba yafi kowa a cikinsu. A’a ya daukesu abokan aiki domin tare aka nadasu kuma tare za suyi aiki na gudanarwa da kuma cigaban Kano Pillars.

    Na fada masa ya rinka kiran yan kwamitinsa taro a duk lokacin da wata matsala ta taso don jin abinda ke bakinsu. Kuma kada ya rinka daukar mataki ko matsaya kai tsaye ba tare da jin ta bakinsu ba.

    Na kuma bashi shawarar kafa kwamitin kwararru ((Technical Committee) don yin aiki tareda masu horar da yan was an kungiyar.

    Anan ne  nace masa zai iya zabo masana wadanda suka kware ya hada da wasu daga cikin yan kwamitinsa don kasancewa yan kwamitin kwararrun.

    Na uku na fada masa cewa ya lura da yadda ake daukar yan wasa a Kano Pillars kuma ya kawo masalaha wadda zata taimakawa Kano Pillars kuma ta taimakawa gwamnati.

    Ta daukar yan wasa nata na kanta kawai kungiyar Kano Pillars zata iya rike kanta kuma ta samawa gwamnati manyan kudade a matsayin kudin shiga a duk lokacin  da zata sayarda dan wasanta ga wata kungiya ko gida ko waje.   

    Na bawa Mai Samba shawarar dakatar da daukar danwasa ko yan wasa na zango daya daga (Agent(s)). Domin ana cutar kungiyar da kuma gwamnati sosai ta wannan bigiren. Na bashi shawarar daukan dan wasa ko yan wasa shekara biyu ko uku.

    Domin ta hakane kawai kungiyar da kuma gwamnatin jihar Kano zasu amfana da kudi masu yawa a duk lokacin da wani dan wasan zai canja sheka zuwa wata kungiyar.

    Na kuma  bashi shawarar zama lafiya da kungiyar magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars. Na fada mahimmancinsu da kuma yi masa nasihar mutuntasu da kuma  daukarsu abokan aiki.

    Ya daukesu abokan aiki kuma ya rinka tuntubarsu lokaci-lokaci don sanin matsalolinsu da kuma taimaka musu sharesu.

     Na nuna masa  amfani da kuma tasirinsu musamman wajen bada goyon bayan da ake so a duk lokacin da Kano Pillars ke wasa gida ko waje.

    Game da mutanenmu yan jarida kuwa na fadawa Mai Samba da suma ya kula dasu da muradunsu. Kada ya bare ya samu matsala dasu.

    Na masa murnar samun mutum biyu a cikin kwamitinsa wadanda aka cemin dukkanninsu kwararrun yan jaridane da kuma bashi shawarar saurararsu don samun daidaito da abokan aikinsu.

    Sai na sake  masa fatan alheri ya juya suka tafi.

    Kicibis
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleNigeria’s poor Paris outing: Minister’s apology not enough
    Next Article Rantsuwar sababbin shugabannin kungiyar Yankasuwar Babban Layi
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

    July 14, 2026

    New Kano Pillars Management: Any hope for real change?

    July 13, 2026

    Gombe Emir’s Cup: Organisers unveil quarter-final fixtures, match dates

    July 10, 2026

    Gombe Emir’s Cup Quarter-Finals set as Eight Clubs progress

    July 8, 2026

    Babangida takes helm of Kano State Sports Commission

    July 6, 2026

    Sports sector reforms: National Sports Commission earns ABU’s praise

    July 6, 2026
    View 1 Comment

    1 Comment

    1. Zahraddeen zakari on August 19, 2024 12:22 pm

      Masha Allah, Allah ya kara taimako

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Free transfer blow: Should Kano Pillars have let Fabian Nworie leave for nothing?

    July 17, 2026

    Katsina Government seeks Kano’s expertise to establish Culture, Reorientation Agency

    July 15, 2026

    NTDA partners Ringo Sport Club for NISPRISPORT 2026

    July 15, 2026

    NASTOCE 2026: Chief Abiodun Odusanwo, Dr. Badaki Aliyu Earn Meritorious Honours

    July 14, 2026

    NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

    July 14, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.