Yan mintuna da bada labarin cewa dan wasan gaba na Kano Pillars Yusuf Abdullahi Tsamage  ya kusa samun nasarar shiga kungiyar wasa a kasar Poland, rahotanni na cewa a yanzu haka Yusuf Tsamage ya dawo gida Nigeria.

A wata hira da Sharif Zaharaddeen Kofar Nasarawa, babban jami’in watsa labarai na kungiyar Kano Pillars  ta wayar tangaraho ya bayyana cewa dan wasa Tsamage ya dawo gida Nigeria shekaran jiya.

Kofar Nasarawa ya kuma tabbatarwa wannan kafa cewa isowarsa gida keda wuya dan wasan ya zarce Abuja saboda gayyatarsa da mai horar da yan wasa na Flying Eagles, Ladan Bosso yayi.

“Ina tabbatar maka cewa Tsamage ya dawo kasa Nigeria kuma a haliin yanzu yana Abuja wajen sansanin horar da yan wasan kungiyar Flying Eagles” cewar Kofar Nasarawa.

Sharif Zaharaddeen Kofar Nasarawa ya kuma shedawa wannan kafa cewa ko jiya Tsamage ne yayi na farko a gasar gudu da akayi tsakanin yan wasan Flying Eagles din.

A cigaba da bibiyarmu don samun labaran wasanni

By Sani Yusif

I was at the production unit of the Triumph Publishing Company, Kano but my keen interest in sports journalism made me to be sports writer and maintained a sports column called (Sports Eye) after my mentor Sani Muhammad Zaria transferred his service to New Nigeria newspapers in Kaduna. And when the government closed the Triumph in 2012, I was transfered to lectured DTP in the Department of Printing Technology of Kano State Polytechnic. And now that I retired, i used to visit the institution weekends for part-time lecturing.