Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

      September 9, 2025

      Gumel, Maizare, others to head newly formed SPS

      August 29, 2025

      Youth Games: For Kano Contingent’s Airs trip, kudos to Gov Abba

      August 27, 2025

      Tataburzar Barau da hukumar wasanni: Yakamata gwamna Abba ya tsawata

      August 18, 2025

      Kano Coaches welcome Bosso back to Kano as he takes up Barau’s TA position

      August 7, 2025
    • Column

      Eagles’ World Cup elimination: Gusau, his associates ought to go

      September 15, 2025

      Sports Develpt in Kano: What Gov Abba should do

      September 8, 2025

      NFF: Using Chelle as scapegoat to cover their shortcomings

      September 1, 2025

      Hosting National Competitions: What’s causing Kano, others to lag behind?

      August 25, 2025

      New season: With two NPFL teams in Kano now

      August 18, 2025
    • News & Media

      Re-Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

      September 11, 2025

      When ASUP beats around the bush

      September 1, 2025

      PPP Plans for Lagos Water Corporation: Groups petition Lagos Assembly

      August 18, 2025

      Mr. President, Yobe girls deserve gifts and recognition as well–Dr. Inuwa

      August 7, 2025

      Immortalization of 22 Dead Athletes: Good, but If I were Governor Abba…

      July 7, 2025
    • Analysis

      Barau FC, please wake up.

      September 15, 2025

      Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

      September 9, 2025

      NPFL matches: Gov Abba backs Barau FC, shames pessimists

      August 23, 2025

      Eunice Chike must be incorporated into Nigeria’s football system immediately

      August 4, 2025

      Power tussle in Pillars: Who is who between  Mai Samba, board and Musa?

      July 16, 2025
    • Personality Profiles

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024

      Dr. Usman Ibrahim Aikawa: New Kano Poly, Director Academic Planning

      January 2, 2024
    Sports Eye
    Home » Hajiya Hauwa Isa Ibrahim: Macen da ta zamanantar da ARTV
    News & Media

    Hajiya Hauwa Isa Ibrahim: Macen da ta zamanantar da ARTV

    Sani YusifBy Sani YusifJuly 31, 2024
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram

    Hajia Hauwa Isa Ibrahim ita ce mai rikon mikamin shugabancin Gidan Talbijin na Abubakar Rimi watau (ARTV Kano) kuma mace ta biyu a tarihin gidan talabijin din da ta rike wannan mukamin.

    Mai girma gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ne ya fara nada ta matsayin mataimakiyar babban manajar gidan talabijin din ARTV, Kafin ya amince zamanta mukaddashin shugaban gidan talabijin na ARTV watau (MD ARTV) din.

    Kafin akai ta ARTV, Hajia Hauwa maaikaciyar gidan radiyon Nasara ce, wanda gushewarta a baro babban gibi saboda kokarinta, aiki tukuru da kuma hangen nesanta a wajen aikinta.

    Tafiyarta zuwa ARTV maaikatan gidan Radiyo Nasara sunyi jimami mai yawa saboda rashin uwa,kawa da kuma abokiyar aiki mara kyamar mutane, mara mugunta da kuma kaunar abokan aikinta.  

    Hajia Huwa mace mai girmama mutane da kuma hangen nesa wadda ta dare  mukamin shugabancin ARTV ne bayan gushewar tsohon shugaban gidan talabijin din wasu lokutan baya.

    Amincewa da mai girma gmamna yayi da nadin nata na zama mai rikon mikamin shugabancin gidan talabijin na ARTV, bai bawa mutane mamaki ba domin sanin cewa ansan zata iya daukar nauyin aikin da aka bata.

    Haka kuma sanin kowane cewa kafin kasancewarta jagoriyar gidan ARTV din, gidan talabijin din nada ko fuskantar matsalolin da  suka taru suka kassara gidan kuma suka hana gidan motsi wanda ya mayarda shi baya.

    Amma darewar Hajia hauwa kan karagar jagorancin gidan keda wuya,  Hajiyar tayi nasarar magance wasu daga cikin manyan matsaloliin gidan, wanda ya kawo tagomashi da kuma farfado dashi daga baccin daya shekara da shekaru yanayi.

    Aikin tukuru da Hajiya Hauwa ta keyiwa gidan ARTV din yasa jamaa da dama dawowa kallo da kuma karin masu kallon shirye-shiryen gidan talabijin din.

    Rashin sakankancewar Hajiyar ya sa ta aiki ba dare ba rana don tabbatar da kawar da tarin matsalolin da suka dabaibaye gidan talabijin din na ARTV mai tarin tarihi.

    Sai dai samun taimakon Allah (SWT) da kuma amincewar mai girma gwamna da  yakeyi mata wajen  sahalewar dukkannin bukatunta na gyara, Hajia Hauwa ta sami nasarori da dama wajen shawo kan wasu daga cikin manyan matsalolin ARTV din.

    Cikin nasarorin da Hajiyar ta samu sun hada da mayarda gidan talabijin na ARTV yin aiki awa 24 kullum ba kamar yadda yake da ba.

    Hajiar tayi nasarar  dora shirye-shiryen gidan talbijin din gabadayansu kan Tauraron Dan Adam na NAGCOMSAT, wanda yasa a halinn yanzu gidan talabijin ARTV ana kallon shirye-shiryensa a duk duniya.

    Hajiyar da kuma inganta ayyukan gidan wajen samarda kayan aiki na zamani a kowane farni ko bangare na gidan ARTV din.

    Hajiyar kuma tana ta kokarin horar da maaikatan gidan iya sarrafa sababbin na’urorin da ta samar a gidan.

    Ba kamar da ba,  yanzu Hajiyar ta gyara na’urorin bada wuta wanda yasa gidan talabijindin ke aiki ko ba wutar NEPA safe da rana.

    Hajiyar kuma ta fara shirin samawa maaikatan gidan talabijin din horo  don kara kwarewa da sanin makamar aiki.

    Don muji yadda mutanen gari da kuma abokan aikinta suke ganin wannan cigaba da takawo, www.sportseye.ng ta zagaya don jin raayin mutane akan yadda suke ko suka ga kokarin Hajia Hauwa Isa Ibrahim akan wannan kujera.

    Hafsat Sani Muhammad, tsohowar shugabar kungiyar mata yan jarida ta Kano watau NAWOJ

    A gaskiya na yaba da kuma jinjinawa kokari da hazakar Hajiya Hauwa  wajen ganin ta canja  akalar gidan talabijin din ARTV.

    Hakika kasancewar Hajia Hauwa  jagoriyar ARTV ya zama alheri domin tarin alherin da ta kawowa gidan da maaikatan gidan baki daya.

    Nasarorin da ta samu yasa gidan talbijin na ARTV da dukkan maaikatan gidan alfahari da  kuma murnar shugabancin Hajia Hauwa saboda tarin cigaban da ta kawowa gidan talabijin din.

    Duk munsan tarin matsaloli da ARTV ke dda shi lokacin da Hajia Hauwa ta zama jagorar gidan, amma fa yanzu duk sun zama tarihi domin ta samawa gidan talbijin na ARTV  kayan aiki na zamani masu  tarin yawa  kuma a kowane farni ko sashe na gidan.

    A ganina dole ne a gode da kuma yabawa mai girman gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf saboda zakulo zakakurar mace irin Hajiya Hauwa da kuma damka mata shugabancin gidan ARTV, wanda  ko kusa bata bawa mara da kunya ba.

    Wannan tasa ya zama dole mu yaba masa saboda gudummawar da yake bata wajen sahalewa da amincewa dukkannin bukatun da ta mikawa ofishinsa.

    Haka kuma dole a yabawa ita Hajia Hauwa bisa kokarinta na horar da maaikatan gidan talabijidin ARTV don kara sanin makamar aiki da kuma kwarewa da sannin yadda za suyi amfani da dukkan naurorin aiki na zamani da shugabancinta ya samar.

    Aisha Miqdad, shugabar ashen mata da kananan yara na radiyon Nasara

    Ni nasan Hajia Hauwa Isa Ibrahim sosai. Macece aminiyar kowa, kuma mai haba-haba da kowa ga kokari ga aiki tukuruu ga kuma rufawa masu aiki a karkashinta asiri.

    Ba tada boye-boye kuma aikin kawai ta sa a gaba. Na yabawa mai girma gwamna daya bata wannan aiki domiin na da tsofaffinn abokan aikinta munsan bazata bamu kunya ba.

    Gashinan kowa yana ganin aikinta a zahiri domin kowa yabawa kkokarinta kawai yake tayi. Dama munsan zata iya kuma gashin ana gani.

    Fatanmu da addu’armu shine ta kara kokari kada ta baiwa maigirma gwamna kunya bisa ga amanarda daya bata.

    Murtala Sale Fagge, Mai Itace

    A gaskiya kasancewar wannan baiwar Allah jagoriyar wannan gida wanda mukafi da sunan  CTV67 a da, wanda a halin yanzu ake kira ARTV ansami cigaba mai tarin yawa.

    Hakika Hajiya Hauwa ta baiwa mara da kunya domin tayi abinda da yawa suka kasa a baya.

    A ganina, ganin shirye-shiryen gidan talabijin din safe, rana da daddare ba karamin cigaba bane kuma abin alfaharine.

    Ina yabawa maai girma gwamna Abba Kabir Yusuf saboda nasarar samo abokiyar aiki. Hakika ita Hajiya macece mai kamar maza…

    Muhammadu Wasilu Kawo, shugaban sashen wasanni na  gidan radiyon Nasara  

    Aganina baiwa Hajia Hauwa aikin mai wuya irin wannan wanda mai girma gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf yayi, abune wanda ya dace saboda sanin kokarinta da jajircewarta wajen aiki da sanin yakamata.

    A   lokacin muke aiki tare a gidan radiyo Nasara, musan Hajiya Hauwa da tsari da kuma aiki tukuro don haka bata wannan mukami abune a hangenmu wanda ya dace.

    A gidan Radiyo Nasara mun san irin kokarinta, juriyarta da hazakarta wajen aiki, don haka cigaban da muke gani yau a ARTV bai bamu mamaki ba.

    Addu’armu Allah ya cigaba da taimakawa kokarinta, ameen.

    da ta zamanartar Haj. Hauwa Macen
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleNadin Mai Samba shugabancin Pillars: Mutanen Kurna sun yabawa AKY
    Next Article Kano Pillars: Now that Mai Samba is on driving seat
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Re-Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

    September 11, 2025

    When ASUP beats around the bush

    September 1, 2025

    PPP Plans for Lagos Water Corporation: Groups petition Lagos Assembly

    August 18, 2025

    Mr. President, Yobe girls deserve gifts and recognition as well–Dr. Inuwa

    August 7, 2025

    Immortalization of 22 Dead Athletes: Good, but If I were Governor Abba…

    July 7, 2025

    Black Saturday: Stakeholders respond to 22 Kano sportsmen death…recommend strategies to prevent its recurrence

    June 16, 2025
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Barau FC, please wake up.

    September 15, 2025

    Eagles’ World Cup elimination: Gusau, his associates ought to go

    September 15, 2025

    Re-Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

    September 11, 2025

    Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

    September 9, 2025

    Sports Develpt in Kano: What Gov Abba should do

    September 8, 2025
    © 2025 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.