Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

      December 3, 2025

      KMC outshines MAKIA to win 2025 NDLEA Chairman’s Cup

      November 23, 2025

      NFF: Collection of underperforming football administrators

      November 17, 2025

      Northwest Varsity Kano shines at NUGA…wins three medals

      November 15, 2025

      … As Female Basketball Team storms Semi-Finals

      November 15, 2025
    • Column

      AFCON 2025: Whither Nigerian referees?

      December 1, 2025

      If Barau can do it, Pillars too can do it

      November 24, 2025

      Disappointing Outing: Sacking Kano Pillars’ Management, not solution

      November 17, 2025

      My Reflections on Adamu’s Kano Pillars’ poor performance views

      November 10, 2025

      Fitness Test: Over 1,500 Referees, Assessors to converge in Kano ‘morrow

      November 7, 2025
    • News & Media

      2025 CIPPON Annual General Meeting (AGM) to Hold in Kano

      November 22, 2025

      Congregation Election: ADUSTECH’s NASU, SSANU candidates triumph

      November 18, 2025

      Retirement: Dantiye congratulates Yakasai

      November 14, 2025

      70th Birthday: Dr. Muhammad Felicitates with Sen. Ibrahim Shekarau

      November 5, 2025

      70th Birthday: Dr. Muhammad Felicitates with Sen. Shekarau

      November 5, 2025
    • Analysis

      Wa ke son ganin bayan su Ali Nayara Mai Samba?

      December 1, 2025

      Now that Pillars has at last broken long-standing jinx…

      November 26, 2025

      To escape relegation: Pillars urged to defeat Ikorodu City

      November 23, 2025

      Kano Pillars FC: Ta yaya muka sami kanmu a haka?

      November 21, 2025

      Jama’a, a ina muka samo ko koyo wannan kuma?

      November 20, 2025
    • Personality Profiles

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024

      Dr. Usman Ibrahim Aikawa: New Kano Poly, Director Academic Planning

      January 2, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Tataburzar Barau da hukumar wasanni: Yakamata gwamna Abba ya tsawata
    Sports News

    Tataburzar Barau da hukumar wasanni: Yakamata gwamna Abba ya tsawata

    Sani YusifBy Sani YusifAugust 18, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    1aa

    A lokacin da kasa Nijeriya da jahohi ke ta kai komo izuwa kasashen waje don samo masu zuba jari a kasa da jahohi baki daya sai gashi a Kano ana kokarin hana kungiyar wasan kwallon kafa ta Barau, kungiyar da bata gwamnati ba yin wasanta na Firimiya a filin wasa na Sani Abacha, Kano.

    Bayan kowa ya sani saboda gazawar kasa Nijeria tare da jahohi wajen samarwa mutanensu aikinyine yasa suke nikan gari zuwa kasashen waje don neman masu zuba jarine don samarwa yan kasa a matakin kasa ko kuma yan jahohi a matakin jahohi aki da abinyi ko kuma bunkasa kasuwancinsu.

    Irin wannan tunaninne wasu daga cikin mutanenmu keyi don samawa matasa maza da mata abinyi wajen bude wasu masana’antu don taimakawa wajen dakile zaman banza a jihohi baki daya.

    Ina tunanin irin wannan tunanin satata Barau yayi wajen kafa kungiyar was an kwallon kafa a jihar kano mai suna Barau Football Club, Kano.

    Kungiyar wadda ta fara a matsayin Barau Academy watau makarantar koyarda wassanni ta rikide ta koma kungiyar kwallon kafa ta kuma suka sami rijistar wasan kasa na NLO daganan suka sami cigaba zuwa NNL sai kuma yanzu suka sake samun cigaba izuwa NPFL duk a cikin dan kankanin lokaci.

    Mutane da yawa sun dauki wannan cigaba ne kuma abin alfahari ga duk wani dan jihar Kano kuma mai kishin Kano domin anyi abin ba sabonba.

    Saidai kuma kash rashin iya siyasa yasa mutanen jihar Kano yiyuwar yin asarar wannan dama da tagomashi da Allah (SWT) yayiwa jihar Kano.

    Duk da a tarihin jihar Kano baa taba samun kungiyoyin wasannin kwallon kafa na rukuni na daya ko Firimiya guda biyu a lokaci dayaba a jihar Kano ba, na dauka gwamnati tare da mutanen jihar Kano baki dayansu za suyi maraba da murna da wannan yanayi.

    Saidai kash dambarwar dake faruwa tsakanin hukumar wasanni ta jihar Kano watau (Sports Commission) da shugabancin kungiyar kwallon Kafa ta Barau akan biyan miliyoyin Nairori kafin sahalewa kungiyar yin wasanta na Firimiya a filin wasa na jihar Kano abin takaicine.

    Kuma wallahi idan aka bari wannan Magana ta fito fili to makwabtanmu da kuma sauran jahohi zasuyi mana dariya kuma su raina tunaninmu.

    Duk da cewa yau yan kwanaki kadan suka rage sabuwar kakar wasa to kasa ta fara aiki, haryanzu an kasa samun mafita domin wata takarda da hukumar wasanni ta jiha ta nuna cewa sai kunkiyar Barau ta biya miliyan hamsin (N50million) kafin a sahale mata yin was anta na Firimiya a filin wasa na Sani Abacha.

    Wannan al’amari  ya daurewa jamaa da dama kai domin an dauka ita hukumar wasanni kamar yadda kowane dan jihar Kano ke ta ya kungiyar Barau murnar shiga gasar Firimiya itama murna zatayi ba yiwa kungiyar zagon kasa ba.

    Wannan shi yasa jamaa da dama ke kira ga gwamnan jihar kano, Alhaji Abba Kabiirr Yusuf da ya tsawatawa ita hukumar wasanni ta jiha tare da ma’aikatar wasanni ta jihar Kano don su sake matsaya domin miliyoyin da sukeso kungiyar kwallon kafa ta Barau ta biya sunyi yawa kuma ba daidai bane.

    Bincike ya nuna cewa ko kungiyar Barau ba ta yan Kano bace kuma baa Kano take ba bai kamata a dora mata harajin biyan irin wannan makudan kudin masu yawaba, balantana Kungiyar Barau kamar ta Kano Pillars da saurran kungiyoyi duk na jihar Kano ne.

    Kamata yayi ita hukumar wasanni da ma’aikatar wasanni su duba taimako da gudummawar da kungiyar Barau tayi tun kafawarta har izuwa yau wajen samarwa matasan jihar Kano aiki da abinyi  ba dora musu harajin miliyan hamsin ba.

    Mutane da dama sun kasa gane hikimar dorawa kunkiyar kwallon kafa ta Barau wannan harraji na miliyan hamsin domin rashin dacewarsa.

    Kamata yayi ita hukumar wasanni da hadin kan ma’aikatar wasanni suyi farin cikin samuwar wannann kungiya da kuma nemo mata tallafi wajen gwamnati don ragewa mai kungiyar radadin tafiyar da kungiyar ba dora musu harajin Naira miliyan hamsin ba.

    Ina kira ga gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf da tsawatawa hukumar wasanni da kuma ma’aikatar wasanni donyin abinda yakamata.

    Bai dace mununa rashin kwarewarmu a fili ba kawai saboda bambamcin siyasa ba. Dukkaninmu yan Kano ne kuma son cigaban Kano mukeyi.

    Idan kunne ya ji…

    da hukumar Dole gwaman kungiyar Barau ta jiha Tataburzar wassanin ya tsawata
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticlePPP Plans for Lagos Water Corporation: Groups petition Lagos Assembly
    Next Article NPFL matches: Gov Abba backs Barau FC, shames pessimists
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

    December 3, 2025

    KMC outshines MAKIA to win 2025 NDLEA Chairman’s Cup

    November 23, 2025

    NFF: Collection of underperforming football administrators

    November 17, 2025

    Northwest Varsity Kano shines at NUGA…wins three medals

    November 15, 2025

    … As Female Basketball Team storms Semi-Finals

    November 15, 2025

    NUGA: BUK makes history following first–ever Volleyball Gold thrilling Final

    November 15, 2025
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

    December 3, 2025

    Wa ke son ganin bayan su Ali Nayara Mai Samba?

    December 1, 2025

    AFCON 2025: Whither Nigerian referees?

    December 1, 2025

    Now that Pillars has at last broken long-standing jinx…

    November 26, 2025

    If Barau can do it, Pillars too can do it

    November 24, 2025
    © 2025 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.