Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      NUGA Games: UniCalabar set to host 28th edition

      January 21, 2026

      KASHIGA elects new officers for two-year term

      January 15, 2026

      Kano Pillars are on course, Says Chairman Mai Samba

      January 11, 2026

      Shake-up in Kano Sports Commission: Chairman, others removed, reassigned

      January 4, 2026

      Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

      December 3, 2025
    • Column

      In defence of BUA’s Super Eagles largess

      January 19, 2026

      Changes needed in Kano State Sports Commission

      January 12, 2026

      DSP Barau, others bag Sportseye 2025 Award

      January 5, 2026

      Northwest Varsity Sports: Key tasks ahead of Prof. Amina S. Bayero

      December 29, 2025

      Sports development in Kano: Expert’s advice

      December 8, 2025
    • News & Media

      Kano Football Coaches host Modern Coaching Seminar for members

      January 7, 2026

      Oseni replaces Ramat as NERC chairman after Senate rejection

      December 19, 2025

      Ahned Musa: Honoring 15 Years of Dedication and Selfless Service

      December 17, 2025

      2025 CIPPON Annual General Meeting (AGM) to Hold in Kano

      November 22, 2025

      Congregation Election: ADUSTECH’s NASU, SSANU candidates triumph

      November 18, 2025
    • Analysis

      As Pillars Return to SAS: What I expect from fans & management

      December 23, 2025

      My Sports Agenda for North-West Development Commission

      December 15, 2025

      Multiple birth dates issues: Where Gombe’s call went off track

      December 11, 2025

      2025 Premier Handball League: Why is Kano absent?

      December 5, 2025

      Wa ke son ganin bayan su Ali Nayara Mai Samba?

      December 1, 2025
    • Personality Profiles

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Tataburzar Barau da hukumar wasanni: Yakamata gwamna Abba ya tsawata
    Sports News

    Tataburzar Barau da hukumar wasanni: Yakamata gwamna Abba ya tsawata

    Sani YusifBy Sani YusifAugust 18, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    1aa

    A lokacin da kasa Nijeriya da jahohi ke ta kai komo izuwa kasashen waje don samo masu zuba jari a kasa da jahohi baki daya sai gashi a Kano ana kokarin hana kungiyar wasan kwallon kafa ta Barau, kungiyar da bata gwamnati ba yin wasanta na Firimiya a filin wasa na Sani Abacha, Kano.

    Bayan kowa ya sani saboda gazawar kasa Nijeria tare da jahohi wajen samarwa mutanensu aikinyine yasa suke nikan gari zuwa kasashen waje don neman masu zuba jarine don samarwa yan kasa a matakin kasa ko kuma yan jahohi a matakin jahohi aki da abinyi ko kuma bunkasa kasuwancinsu.

    Irin wannan tunaninne wasu daga cikin mutanenmu keyi don samawa matasa maza da mata abinyi wajen bude wasu masana’antu don taimakawa wajen dakile zaman banza a jihohi baki daya.

    Ina tunanin irin wannan tunanin satata Barau yayi wajen kafa kungiyar was an kwallon kafa a jihar kano mai suna Barau Football Club, Kano.

    Kungiyar wadda ta fara a matsayin Barau Academy watau makarantar koyarda wassanni ta rikide ta koma kungiyar kwallon kafa ta kuma suka sami rijistar wasan kasa na NLO daganan suka sami cigaba zuwa NNL sai kuma yanzu suka sake samun cigaba izuwa NPFL duk a cikin dan kankanin lokaci.

    Mutane da yawa sun dauki wannan cigaba ne kuma abin alfahari ga duk wani dan jihar Kano kuma mai kishin Kano domin anyi abin ba sabonba.

    Saidai kuma kash rashin iya siyasa yasa mutanen jihar Kano yiyuwar yin asarar wannan dama da tagomashi da Allah (SWT) yayiwa jihar Kano.

    Duk da a tarihin jihar Kano baa taba samun kungiyoyin wasannin kwallon kafa na rukuni na daya ko Firimiya guda biyu a lokaci dayaba a jihar Kano ba, na dauka gwamnati tare da mutanen jihar Kano baki dayansu za suyi maraba da murna da wannan yanayi.

    Saidai kash dambarwar dake faruwa tsakanin hukumar wasanni ta jihar Kano watau (Sports Commission) da shugabancin kungiyar kwallon Kafa ta Barau akan biyan miliyoyin Nairori kafin sahalewa kungiyar yin wasanta na Firimiya a filin wasa na jihar Kano abin takaicine.

    Kuma wallahi idan aka bari wannan Magana ta fito fili to makwabtanmu da kuma sauran jahohi zasuyi mana dariya kuma su raina tunaninmu.

    Duk da cewa yau yan kwanaki kadan suka rage sabuwar kakar wasa to kasa ta fara aiki, haryanzu an kasa samun mafita domin wata takarda da hukumar wasanni ta jiha ta nuna cewa sai kunkiyar Barau ta biya miliyan hamsin (N50million) kafin a sahale mata yin was anta na Firimiya a filin wasa na Sani Abacha.

    Wannan al’amari  ya daurewa jamaa da dama kai domin an dauka ita hukumar wasanni kamar yadda kowane dan jihar Kano ke ta ya kungiyar Barau murnar shiga gasar Firimiya itama murna zatayi ba yiwa kungiyar zagon kasa ba.

    Wannan shi yasa jamaa da dama ke kira ga gwamnan jihar kano, Alhaji Abba Kabiirr Yusuf da ya tsawatawa ita hukumar wasanni ta jiha tare da ma’aikatar wasanni ta jihar Kano don su sake matsaya domin miliyoyin da sukeso kungiyar kwallon kafa ta Barau ta biya sunyi yawa kuma ba daidai bane.

    Bincike ya nuna cewa ko kungiyar Barau ba ta yan Kano bace kuma baa Kano take ba bai kamata a dora mata harajin biyan irin wannan makudan kudin masu yawaba, balantana Kungiyar Barau kamar ta Kano Pillars da saurran kungiyoyi duk na jihar Kano ne.

    Kamata yayi ita hukumar wasanni da ma’aikatar wasanni su duba taimako da gudummawar da kungiyar Barau tayi tun kafawarta har izuwa yau wajen samarwa matasan jihar Kano aiki da abinyi  ba dora musu harajin miliyan hamsin ba.

    Mutane da dama sun kasa gane hikimar dorawa kunkiyar kwallon kafa ta Barau wannan harraji na miliyan hamsin domin rashin dacewarsa.

    Kamata yayi ita hukumar wasanni da hadin kan ma’aikatar wasanni suyi farin cikin samuwar wannann kungiya da kuma nemo mata tallafi wajen gwamnati don ragewa mai kungiyar radadin tafiyar da kungiyar ba dora musu harajin Naira miliyan hamsin ba.

    Ina kira ga gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf da tsawatawa hukumar wasanni da kuma ma’aikatar wasanni donyin abinda yakamata.

    Bai dace mununa rashin kwarewarmu a fili ba kawai saboda bambamcin siyasa ba. Dukkaninmu yan Kano ne kuma son cigaban Kano mukeyi.

    Idan kunne ya ji…

    da hukumar Dole gwaman kungiyar Barau ta jiha Tataburzar wassanin ya tsawata
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticlePPP Plans for Lagos Water Corporation: Groups petition Lagos Assembly
    Next Article NPFL matches: Gov Abba backs Barau FC, shames pessimists
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    NUGA Games: UniCalabar set to host 28th edition

    January 21, 2026

    KASHIGA elects new officers for two-year term

    January 15, 2026

    Kano Pillars are on course, Says Chairman Mai Samba

    January 11, 2026

    Shake-up in Kano Sports Commission: Chairman, others removed, reassigned

    January 4, 2026

    Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

    December 3, 2025

    KMC outshines MAKIA to win 2025 NDLEA Chairman’s Cup

    November 23, 2025
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    How Northwest Varsity blocked my chance to study Law with Emir Sanusi

    January 22, 2026

    NUGA Games: UniCalabar set to host 28th edition

    January 21, 2026

    In defence of BUA’s Super Eagles largess

    January 19, 2026

    KASHIGA elects new officers for two-year term

    January 15, 2026

    Changes needed in Kano State Sports Commission

    January 12, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.