Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Kungiyar Barau: Kuskuren da Ibrahim Canji, mabiyansa suka tafka

      September 30, 2025

      Sauye-sayen kungiyar Barau: Kuskuren Sanata Barau tare dana Canji

      September 25, 2025

      Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

      September 9, 2025

      Gumel, Maizare, others to head newly formed SPS

      August 29, 2025

      Youth Games: For Kano Contingent’s Airs trip, kudos to Gov Abba

      August 27, 2025
    • Column

      SWAN: Genuine sports stakeholder than NFF, other federation members

      October 6, 2025

      Changes in Barau FC: Where DSP Barau Jibrin fumbles

      September 29, 2025

      Shehu Dikko one year in office: Is there light in the tunnel?

      September 22, 2025

      Eagles’ World Cup elimination: Gusau, his associates ought to go

      September 15, 2025

      Sports Develpt in Kano: What Gov Abba should do

      September 8, 2025
    • News & Media

      Re-Extortion at Urology Center: Gov Abba must hear this

      October 10, 2025

      Environmental Journalists begin two-day training in Abuja

      September 23, 2025

      Two-day training for environment journalists in Abuja

      September 21, 2025

      To transform smart living in Nigeria: FENAC secure solutions, collaborates with South African firm

      September 17, 2025

      Re-Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

      September 11, 2025
    • Analysis

      Rashin kokarin Kano Pillars da Barau: Sai fa gwamnati ta yi wani abu

      October 7, 2025

      Barau FC, please wake up.

      September 15, 2025

      Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

      September 9, 2025

      NPFL matches: Gov Abba backs Barau FC, shames pessimists

      August 23, 2025

      Eunice Chike must be incorporated into Nigeria’s football system immediately

      August 4, 2025
    • Personality Profiles

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024

      Dr. Usman Ibrahim Aikawa: New Kano Poly, Director Academic Planning

      January 2, 2024
    Sports Eye
    Home » Sauye-sayen kungiyar Barau: Kuskuren Sanata Barau tare dana Canji
    Sports News

    Sauye-sayen kungiyar Barau: Kuskuren Sanata Barau tare dana Canji

    Sani YusifBy Sani YusifSeptember 25, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    Barau

    A yanzu dai ta fito fili cewa akwai tirka tirkar shugabanci babba a kungiyar kwallon kafa ta Barau wadda ita ce ta kawo sauye sayen shugabanci da aka gudanar a kungiyar a makon da ya gabata.

    Wanda a makon bayanne aka bayyana nadin tsohon shugaban kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars kuma tsohon mai bawa gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje shawara kan harkokin wasanni, Alhaji Kabiru Baita a matsayin mataimakin shugaban kungiyar ta Barau watan (Vice President).

    Haka kuma an bayyana nadin tsohon shugaban kungiyar kwallon kafa ta Lobi, Dominic Iofa a matsayin manajan gudanarwar kungiyar.

    Tun bayyana wadannan sababbin canje-canjen aka ta jin cece kuce da maganganu tsakanin magoya baya da kuma wasu daga cikin tsofaffin shuganbannin kungiyar ta Barau.

    Wasu na ganin cewa yin canje-canjen a wannen lokacin kamar cin fuska ne ko kuma nuna gazawar tsofaffin shugabannin kungiyarne karkashin Ibrahim Canji duk da kokarinsu na baya.

    Amma wasu na ganin daidai da maanar yin canjin domin gazawar shugabancin Ibrahim Canji da mukarrabansa ya fito fili tun fara wasan gasar firimiya ta kasa.

    Samun maki biyu kacal daga wasanni hudu ne ya nuna ko fito da rashin fahimta ko kwarewar shugabancin Ibrahim Canji a kungiyar Barau kuma shine ya bada damar yin garambawul din shugabancin kungiyar.

    Kowa yasan garanbawul bazai tabbata ba sai anyi binciken abubuwan dake faruwa a cikin kungiyar wanda ya sa ta tangal tangal a babban gasar kwallon kafa ta kasar nan.

    Bincikenne ya nuna wasu irin zarge zagen son zuciya masu muni na gaftarewa yan wasan kungiyar albashinsu mai yawa a kowane wata.

    To ni a ganina ba bawanda zaa zarga a wannan mumunan katobara irin shi mai kungiyar watau Sanata Barau Jibrin.

    Saboda yadda ya dauki harkar kungiyar ya dankawa mutum daya wato Ibrahin Canji shi kadai, abinda yasashi cin karensa ba babbaka.

    Koda yake naji Muktari Zico a wata fira da gidan Radiyo Nasara yana cewa yana daya daga cikin yan majalisar gudanarwar kungiyar, amma hakan bai hana abinda ake zargi ba.

    Kowa yasan cewa idan kungiya nada kwamitin gudanarwa mai karfi to sune wuka sune nama wajen tafiyar da kungiyar ba mutum daya ba.

    Kuma zai hana mutum daya daga cikin wadannan mutanen yin yadda yake so domin sai dukannin yan kwamiti sun amince zaa tafiyar da komai.

    Amma baiwa mutum daya dama shi kadai ba karamin kuskure bane musamman idan aka duba irin yawan kudin da shi Sanata Barau yake turawa cikin kungiyar.

    Amma tunda an farga an bayyana sababbin canje-canje, yakamata asa ido kuma abar kowa yayi aikin da ya kamaceshi ba tare da masa shishshigi ba. Amma fa wannan bazai hana bincike da sa ido ba don tabbatar da kowa yanayin aikinsa daidai bason zuciya.

    Wani kuskure ko kuma abinda aka manta shine wasan kwallon kafa a Nijerya ba a fili kawai akeyin saba. Akwai wasu abubuwa da akeyi a bayan fage wanda mutumin da bai saniba bazai saniba.

    Ina ganin rashin sanin irin wannan kinayar ne nasu Ibrahim Canji da mukarrabensa ya jefa kungiyar Barau cikin hahin da take ciki a yau.

    Amma mutane da dama sunyi farin cikin wannan farkawa da Mai gima Sanat yayi saidai kuma sunyi mamakin ganin sunan irinsu tsohon shugaban kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, Hon.Kabiru Baita da Dominic Iofa a cikin sabon tsarin kungiyar.

    Mamakin da mutane sukeyi shine me yasa duk fadi da girman jihar Kano  baaga kowaba sai Kabiru Baita da Dominic?

    Wani abin haushi shi Dominic Iofa, mutum ne da ake zargi da ruguza kungiyar kwallon kafa ta Lobi dake garinsu dake Makurdi.

    Da Baita da Dominic a jamaa da dama na ganin lokacinsu ya wuce domin basu da wani tarihi da suka bari a baya wanda zaisa ayi musu kallon masu nasara balantana a zaci nasara a garesu.

    Wallahi tallahi a cikin garinnan namu na Kano akwai zakwakurin mutane masu hazaka da basirar da zasuyi abinda Baita da Dominic bazasu iyaba idan an basu dama.

    Mutane da dama na ganin idan da gaske shi mai girma Sanata Barau yake, kamata yayi ya duba sosai ko kuma yasa ayi masa binciken na mzakwakuran mutane do zakulo masu ilmi da sannin harkar don basu damar tafi da kungiyar ba Baita da Dominic ba.

    Munga gazawarsu a baya lokacin shugancinsu a kungiyoyinsu na baya na Kano Pillars da Lobi Stars don haka jammaa da dama sun zaci wasu daban.

    Amma tunda an riga malam zuwa masallaci, yakamata su su Baita da Dominic suji tsoron Allah wajen yin duk abinda zaayi domin kungiyar Barau ta cigaba.

    Su sani wannan kungiyar bata gwamnati bace don haka kada susa son zuciya irin wanda sukayi a baya wajen tafiyan da kungiyoyin Kano Pillars da Lobi a baya.

    Su taimakawa kungiyar wajen samun madogara don samun kudin shiga masu yawa don rage bani bani wajen Sanita Barau.

    Su tabbatar duk dan wasan da kungiyar zata dauka bana aro bane don idan ya tashi tafiya gaba, kungiyar Barau ta sami kudin shiga ba shiiga cikin aljihunsu dana dillalin yan wasa ba.

    Su kafa Kwamitin Kwararru (Technical Committee) don taimakawa maihorarrwa samo yan wasan da kungiyar take cewa bata dasu da kuma tafiyar da kungiyar.

    Kamar yadda na fada a baya cikin wani rubutu na, su duba makwabta Ghana, Niger, Kamaru da sauransu don samun yan wasan da zasu taimakawa kungiyar farfadowa.

    A karshe, su sani cewa ciyarda kungiyar kwallon kafa ta Barau gaba shine ciyarda jihar Kano gaba.

    Ina musu fatan alheri

     

    kungiyar Barau Laifin Rikicin Sanata Barau ne shuabancin
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleEnvironmental Journalists begin two-day training in Abuja
    Next Article Changes in Barau FC: Where DSP Barau Jibrin fumbles
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Kungiyar Barau: Kuskuren da Ibrahim Canji, mabiyansa suka tafka

    September 30, 2025

    Kano Pillars three games, one point: Stakeholders react

    September 9, 2025

    Gumel, Maizare, others to head newly formed SPS

    August 29, 2025

    Youth Games: For Kano Contingent’s Airs trip, kudos to Gov Abba

    August 27, 2025

    Tataburzar Barau da hukumar wasanni: Yakamata gwamna Abba ya tsawata

    August 18, 2025

    Kano Coaches welcome Bosso back to Kano as he takes up Barau’s TA position

    August 7, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Re-Extortion at Urology Center: Gov Abba must hear this

    October 10, 2025

    Extortion at Urology Center: Gov Abba must hear this

    October 9, 2025

    Rashin kokarin Kano Pillars da Barau: Sai fa gwamnati ta yi wani abu

    October 7, 2025

    SWAN: Genuine sports stakeholder than NFF, other federation members

    October 6, 2025

    Kungiyar Barau: Kuskuren da Ibrahim Canji, mabiyansa suka tafka

    September 30, 2025
    © 2025 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.