Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

      July 14, 2026

      New Kano Pillars Management: Any hope for real change?

      July 13, 2026

      Gombe Emir’s Cup: Organisers unveil quarter-final fixtures, match dates

      July 10, 2026

      Gombe Emir’s Cup Quarter-Finals set as Eight Clubs progress

      July 8, 2026

      Babangida takes helm of Kano State Sports Commission

      July 6, 2026
    • Column

      Has Barau FC management lost sight of Senator Barau’s vision?

      July 24, 2026

      Free transfer blow: Should Kano Pillars have let Fabian Nworie leave for nothing?

      July 17, 2026

      With full government support, Babangida, Maizare, others must produce results

      July 10, 2026

      Gov. Abba’s listening approach: Key to reviving Kano Pillars, Kano Sports Commission

      July 3, 2026

      Kano State Sports under siege: Governor Abba must hear it

      June 26, 2026
    • News & Media

      Keyamo, Musawa confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

      July 24, 2026

      Keyamo, Musawa Confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

      July 24, 2026

      Katsina Government seeks Kano’s expertise to establish Culture, Reorientation Agency

      July 15, 2026

      NTDA partners Ringo Sport Club for NISPRISPORT 2026

      July 15, 2026

      NASTOCE 2026: Chief Abiodun Odusanwo, Dr. Badaki Aliyu Earn Meritorious Honours

      July 14, 2026
    • Analysis

      Kano Sports: Huge expectations for new Kano Pillars, Sports Commission Boards

      June 29, 2026

      Kano Pillars’ survival hopes alive despite tough battle ahead

      May 22, 2026

      NPFL survival at stake: Relegation battle heads into final day

      May 14, 2026

      Kano Pillars: Final words before crucial Plateau United FC encounter

      May 12, 2026

      Alleged Bias in Kano Sports Support: What Kano FA Should Address

      May 5, 2026
    • Personality Profiles

      Engr. Aikawa assumes Office as pioneer Deputy Rector (Academics)

      July 6, 2026

      Making of a Leader: Dr. Garba A. Adamu’s journey from laboratory to leadership

      July 4, 2026

      AbdulGaffar I. Dawakin Tofa: Shaping public discourse through journalism, broadcasting

      June 24, 2026

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Sauye-sayen kungiyar Barau: Kuskuren Sanata Barau tare dana Canji
    Sports News

    Sauye-sayen kungiyar Barau: Kuskuren Sanata Barau tare dana Canji

    Sani YusifBy Sani YusifSeptember 25, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    Barau

    A yanzu dai ta fito fili cewa akwai tirka tirkar shugabanci babba a kungiyar kwallon kafa ta Barau wadda ita ce ta kawo sauye sayen shugabanci da aka gudanar a kungiyar a makon da ya gabata.

    Wanda a makon bayanne aka bayyana nadin tsohon shugaban kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars kuma tsohon mai bawa gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje shawara kan harkokin wasanni, Alhaji Kabiru Baita a matsayin mataimakin shugaban kungiyar ta Barau watan (Vice President).

    Haka kuma an bayyana nadin tsohon shugaban kungiyar kwallon kafa ta Lobi, Dominic Iofa a matsayin manajan gudanarwar kungiyar.

    Tun bayyana wadannan sababbin canje-canjen aka ta jin cece kuce da maganganu tsakanin magoya baya da kuma wasu daga cikin tsofaffin shuganbannin kungiyar ta Barau.

    Wasu na ganin cewa yin canje-canjen a wannen lokacin kamar cin fuska ne ko kuma nuna gazawar tsofaffin shugabannin kungiyarne karkashin Ibrahim Canji duk da kokarinsu na baya.

    Amma wasu na ganin daidai da maanar yin canjin domin gazawar shugabancin Ibrahim Canji da mukarrabansa ya fito fili tun fara wasan gasar firimiya ta kasa.

    Samun maki biyu kacal daga wasanni hudu ne ya nuna ko fito da rashin fahimta ko kwarewar shugabancin Ibrahim Canji a kungiyar Barau kuma shine ya bada damar yin garambawul din shugabancin kungiyar.

    Kowa yasan garanbawul bazai tabbata ba sai anyi binciken abubuwan dake faruwa a cikin kungiyar wanda ya sa ta tangal tangal a babban gasar kwallon kafa ta kasar nan.

    Bincikenne ya nuna wasu irin zarge zagen son zuciya masu muni na gaftarewa yan wasan kungiyar albashinsu mai yawa a kowane wata.

    To ni a ganina ba bawanda zaa zarga a wannan mumunan katobara irin shi mai kungiyar watau Sanata Barau Jibrin.

    Saboda yadda ya dauki harkar kungiyar ya dankawa mutum daya wato Ibrahin Canji shi kadai, abinda yasashi cin karensa ba babbaka.

    Koda yake naji Muktari Zico a wata fira da gidan Radiyo Nasara yana cewa yana daya daga cikin yan majalisar gudanarwar kungiyar, amma hakan bai hana abinda ake zargi ba.

    Kowa yasan cewa idan kungiya nada kwamitin gudanarwa mai karfi to sune wuka sune nama wajen tafiyar da kungiyar ba mutum daya ba.

    Kuma zai hana mutum daya daga cikin wadannan mutanen yin yadda yake so domin sai dukannin yan kwamiti sun amince zaa tafiyar da komai.

    Amma baiwa mutum daya dama shi kadai ba karamin kuskure bane musamman idan aka duba irin yawan kudin da shi Sanata Barau yake turawa cikin kungiyar.

    Amma tunda an farga an bayyana sababbin canje-canje, yakamata asa ido kuma abar kowa yayi aikin da ya kamaceshi ba tare da masa shishshigi ba. Amma fa wannan bazai hana bincike da sa ido ba don tabbatar da kowa yanayin aikinsa daidai bason zuciya.

    Wani kuskure ko kuma abinda aka manta shine wasan kwallon kafa a Nijerya ba a fili kawai akeyin saba. Akwai wasu abubuwa da akeyi a bayan fage wanda mutumin da bai saniba bazai saniba.

    Ina ganin rashin sanin irin wannan kinayar ne nasu Ibrahim Canji da mukarrabensa ya jefa kungiyar Barau cikin hahin da take ciki a yau.

    Amma mutane da dama sunyi farin cikin wannan farkawa da Mai gima Sanat yayi saidai kuma sunyi mamakin ganin sunan irinsu tsohon shugaban kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, Hon.Kabiru Baita da Dominic Iofa a cikin sabon tsarin kungiyar.

    Mamakin da mutane sukeyi shine me yasa duk fadi da girman jihar Kano  baaga kowaba sai Kabiru Baita da Dominic?

    Wani abin haushi shi Dominic Iofa, mutum ne da ake zargi da ruguza kungiyar kwallon kafa ta Lobi dake garinsu dake Makurdi.

    Da Baita da Dominic a jamaa da dama na ganin lokacinsu ya wuce domin basu da wani tarihi da suka bari a baya wanda zaisa ayi musu kallon masu nasara balantana a zaci nasara a garesu.

    Wallahi tallahi a cikin garinnan namu na Kano akwai zakwakurin mutane masu hazaka da basirar da zasuyi abinda Baita da Dominic bazasu iyaba idan an basu dama.

    Mutane da dama na ganin idan da gaske shi mai girma Sanata Barau yake, kamata yayi ya duba sosai ko kuma yasa ayi masa binciken na mzakwakuran mutane do zakulo masu ilmi da sannin harkar don basu damar tafi da kungiyar ba Baita da Dominic ba.

    Munga gazawarsu a baya lokacin shugancinsu a kungiyoyinsu na baya na Kano Pillars da Lobi Stars don haka jammaa da dama sun zaci wasu daban.

    Amma tunda an riga malam zuwa masallaci, yakamata su su Baita da Dominic suji tsoron Allah wajen yin duk abinda zaayi domin kungiyar Barau ta cigaba.

    Su sani wannan kungiyar bata gwamnati bace don haka kada susa son zuciya irin wanda sukayi a baya wajen tafiyan da kungiyoyin Kano Pillars da Lobi a baya.

    Su taimakawa kungiyar wajen samun madogara don samun kudin shiga masu yawa don rage bani bani wajen Sanita Barau.

    Su tabbatar duk dan wasan da kungiyar zata dauka bana aro bane don idan ya tashi tafiya gaba, kungiyar Barau ta sami kudin shiga ba shiiga cikin aljihunsu dana dillalin yan wasa ba.

    Su kafa Kwamitin Kwararru (Technical Committee) don taimakawa maihorarrwa samo yan wasan da kungiyar take cewa bata dasu da kuma tafiyar da kungiyar.

    Kamar yadda na fada a baya cikin wani rubutu na, su duba makwabta Ghana, Niger, Kamaru da sauransu don samun yan wasan da zasu taimakawa kungiyar farfadowa.

    A karshe, su sani cewa ciyarda kungiyar kwallon kafa ta Barau gaba shine ciyarda jihar Kano gaba.

    Ina musu fatan alheri

     

    kungiyar Barau Laifin Rikicin Sanata Barau ne shuabancin
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleEnvironmental Journalists begin two-day training in Abuja
    Next Article Changes in Barau FC: Where DSP Barau Jibrin fumbles
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

    July 14, 2026

    New Kano Pillars Management: Any hope for real change?

    July 13, 2026

    Gombe Emir’s Cup: Organisers unveil quarter-final fixtures, match dates

    July 10, 2026

    Gombe Emir’s Cup Quarter-Finals set as Eight Clubs progress

    July 8, 2026

    Babangida takes helm of Kano State Sports Commission

    July 6, 2026

    Sports sector reforms: National Sports Commission earns ABU’s praise

    July 6, 2026
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Keyamo, Musawa confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

    July 24, 2026

    Keyamo, Musawa Confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

    July 24, 2026

    Has Barau FC management lost sight of Senator Barau’s vision?

    July 24, 2026

    Free transfer blow: Should Kano Pillars have let Fabian Nworie leave for nothing?

    July 17, 2026

    Katsina Government seeks Kano’s expertise to establish Culture, Reorientation Agency

    July 15, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.