Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

      December 3, 2025

      KMC outshines MAKIA to win 2025 NDLEA Chairman’s Cup

      November 23, 2025

      NFF: Collection of underperforming football administrators

      November 17, 2025

      Northwest Varsity Kano shines at NUGA…wins three medals

      November 15, 2025

      … As Female Basketball Team storms Semi-Finals

      November 15, 2025
    • Column

      Sports development in Kano: Expert’s advice

      December 8, 2025

      AFCON 2025: Whither Nigerian referees?

      December 1, 2025

      If Barau can do it, Pillars too can do it

      November 24, 2025

      Disappointing Outing: Sacking Kano Pillars’ Management, not solution

      November 17, 2025

      My Reflections on Adamu’s Kano Pillars’ poor performance views

      November 10, 2025
    • News & Media

      Oseni replaces Ramat as NERC chairman after Senate rejection

      December 19, 2025

      Ahned Musa: Honoring 15 Years of Dedication and Selfless Service

      December 17, 2025

      2025 CIPPON Annual General Meeting (AGM) to Hold in Kano

      November 22, 2025

      Congregation Election: ADUSTECH’s NASU, SSANU candidates triumph

      November 18, 2025

      Retirement: Dantiye congratulates Yakasai

      November 14, 2025
    • Analysis

      My Sports Agenda for North-West Development Commission

      December 15, 2025

      Multiple birth dates issues: Where Gombe’s call went off track

      December 11, 2025

      2025 Premier Handball League: Why is Kano absent?

      December 5, 2025

      Wa ke son ganin bayan su Ali Nayara Mai Samba?

      December 1, 2025

      Now that Pillars has at last broken long-standing jinx…

      November 26, 2025
    • Personality Profiles

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Canjin shugabannin Kano Pillars: Ba shi bane mafita
    Sports News

    Canjin shugabannin Kano Pillars: Ba shi bane mafita

    Sani YusifBy Sani YusifNovember 5, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    1a

    Tun lokacin da al’amuran kungiyar Kano Pillars suka shiga wani hali marasa kyau da dadin ji saboda rashin nasarar da kungiyar keyi a gasar pirimiya ta kasa watau NPFL, wasu da dama nata kiraye-kirayin rushe hukumar gudanarwar kungiyar.

    Wasu na ganin cewa tunda shugabannin Kano Pillars sun kasa dauka da sauke nauyin da gwamnati ta dora musu, yakamata gwamnati ta rushesu da kuma sauyasu da wasu.

    Wani rahoto ya nuna cewa tun fara jin irin wadanan kiraye-kiraye ne mutane dabam-dabam masu son mukamin shugabancin kungiyar  ke ta  tururruwar da dafdala wasu a offishi wasu kuma a gidan kwamishinan matasa da wasanni, Hon. Mustapha Rabiu Kwankwaso don samun amincewarsa na zama daya daga cikin shugabannin kungiyar.

    Wasu kuma wadanda basu da dama ko fada a wajen kwamishina Kwankwaso rahotanni ya nuna cewa suna bin jigajigai da manyan jami’en gwamnati dana jamiyyar NNPP don samun zama daya daga cikin yan kwamitin gudanarwar kungiyar ta Kano Pillars.

    Wasu ma a cewar wata kafar, dunguma zuwa ofishin mataimakin gwamna, kwamraid Aminu Abdussalamu Gwarzo sukayi don sashi ya saka baki wajen tabbatar da samun mukaman kungiyar Kano Pillars din.

    Rahoto ya kuka nuna cewa cikin masuyin zarya zuwa ofishin kwamishina Kwankwaso kullun-kullun don neman shugabancin Kano Pillars din, akwai daya daga cikin tsofaffin shugabannin kungiyar.

    Haka kuma rahotanni sun nuna akwai kuma wasu daga cikin tsofaffin yan kwamitin gudanarwar kungiyar na baya wadanda suke ta shishshigewa kwamishina don samun matsayi a kungiyar Kano Pillars din.

    Wani rahoton kuma ya bayyana cewa hatta wasu daga cikin yan kwamitin gudanarwar kungiyar masu ci yanzu na daga cikin masu nema idan an rushesu, to a basu dama domin suna ganin suna da yadda za suyi tagomashin kungiyar ya dawo.

    Amma saidai a lokacin da wasu mutanen ke ganin cewa canjin shugabancin kungiyarne kawai mafita, mu aganinmu canjin ba shi bane a’ala domin a baya da aka sami kai cikin irin wannan yanayin, anyi canjin amma baiyi wani tasiri ba.

    Nan baya kadan irin wannan ibtala’in ya taba fadawa kungiyar wanda yasa gwamnatin baya rushe hukumar gudanarwar kungiyarkarkashin shugabancin Jibrin Jambul da kuma bawa tsohon shugaban hukumar wasanni ta Kano, Alhaji Ibrahim Galadima ragamar gudanar da kungiyar wanda babu abinda ya sauya.

    A karshe ma dai sai da kungiyar ta fado matsayi na kasa na NNL kafin sabuwar gwamnati ta shigo kuma aka samu kungiyar ta komo matsayinta na yanzu.

    A ganinmu kamata yayi gwamnati ta fara kafa kwamiti na masana don bin ciko dalilai da abubuwan dake damun kungiyar sannan abi abubuwan da suka zayyana daya bayan daya don mayarda kungiyar tsayawa da kafafunta.

    A kullum muna fada cewa idan anaso kungiyar Kano Pillar tayi abinda akeso to sai an mata abinda yakamata.

    Abu na farko da zaayi shine ayi ko a tafiyar ko gudanar da ita yadda ake gudanar da sauran kungiyoyi kwallon kafa a sauran jahohi ko kuma kasashe na fadin duniya.

    Irin yadda gwamnati ke bawa kungiyar Kano Pillars kudi don gudanar da harkokin kungiyar gutsi-gutsi ko guntu-guntu  ba daidai bane kuma ba tsari a ciki.

    Yin hakan na hana shugabannin kungiyar samun nutsuwa da hangen nesa  da kuma shiri da wuri don gudanar da ayyukan kungiyar.

    Akoda yaushe muna bada shawarar duba kasafin kudin kungiyar na shekara da kuma amincewa da shi, wanda daga nan sai a sakar musu kudi gwargwadon iko  don su cigaba da gudanar da harkokinsu ba tare da zuwa wajen gwamnati sati-sati ba don karbar kudin tafiya ko kuma shirin wasan gida ba.

    Ina tabbatar muku cewa babu wata kungiyar da ake gudanar da ita yadda ake gudanar da Kano Pillars a fadin kasarnan baki daya. Wannan shine abu na farkpo da gwamnati zata gyara idan anaso aga kokarin kungiyar nan gaba.

    Ko zuwa wasan da kungiyar da tayi na baya-bayannan zuwau garin Aba, wasansu da Enyinba baa sallamesu sun tafi da wuri ba duk da nisan garin domin sai ranar Jumaa suka tafi wasan da za suyi ranar Lahadi. Ta yaya akeso aga da kyau da irin wannan tsarin?

    Kaucewa irin wannan lamari da yanayi ne kadai zai ceci kungiyar Kano Pillars ba wai canje-canjen shugabannin kungiyar ba.

    Domin bincike ya nuna cewa yawancin masu so da neman mukamin shugabancin kungiyar ba wani abu na musamman garesu ga kungiyarba sai dai son abin duniya da tarin son zuciyarsu kawai.

    Kamar yadda na zayyana a cikin wannan rubutun, kamata yayi gwamnati ta fara neman shawarar masana don sanin yadda zaa fidda kungiyar daga cikin wannan mummunan hali da ta shiga ba canjin shugabanciba.

    Allah yabamu saa, amen.

    Kano Pillars Rushe shugabancin
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleHappy birthday, Magistrate (Coach) Ibrahim Gwadabe
    Next Article NUGA Games: Northwest Varsity Departs, Poised for Excellence
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Kamata yayi Pillars su sa kulunboto a bayansu

    December 3, 2025

    KMC outshines MAKIA to win 2025 NDLEA Chairman’s Cup

    November 23, 2025

    NFF: Collection of underperforming football administrators

    November 17, 2025

    Northwest Varsity Kano shines at NUGA…wins three medals

    November 15, 2025

    … As Female Basketball Team storms Semi-Finals

    November 15, 2025

    NUGA: BUK makes history following first–ever Volleyball Gold thrilling Final

    November 15, 2025
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Oseni replaces Ramat as NERC chairman after Senate rejection

    December 19, 2025

    Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

    December 19, 2025

    Ahned Musa: Honoring 15 Years of Dedication and Selfless Service

    December 17, 2025

    My Sports Agenda for North-West Development Commission

    December 15, 2025

    Multiple birth dates issues: Where Gombe’s call went off track

    December 11, 2025
    © 2025 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.