Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

      July 14, 2026

      New Kano Pillars Management: Any hope for real change?

      July 13, 2026

      Gombe Emir’s Cup: Organisers unveil quarter-final fixtures, match dates

      July 10, 2026

      Gombe Emir’s Cup Quarter-Finals set as Eight Clubs progress

      July 8, 2026

      Babangida takes helm of Kano State Sports Commission

      July 6, 2026
    • Column

      With full government support, Babangida, Maizare, others must produce results

      July 10, 2026

      Gov. Abba’s listening approach: Key to reviving Kano Pillars, Kano Sports Commission

      July 3, 2026

      Kano State Sports under siege: Governor Abba must hear it

      June 26, 2026

      Madrid, Barcelona Supporters’ friendly meeting in Kano: A welcome initiative, but…

      June 19, 2026

      2026 World Cup Qualifiers: Where I disagree with Gara-Gombe’s position

      June 12, 2026
    • News & Media

      Katsina Government seeks Kano’s expertise to establish Culture, Reorientation Agency

      July 15, 2026

      NTDA partners Ringo Sport Club for NISPRISPORT 2026

      July 15, 2026

      NASTOCE 2026: Chief Abiodun Odusanwo, Dr. Badaki Aliyu Earn Meritorious Honours

      July 14, 2026

      To Reposition Broadcasting in Nigeria: BON constitutes Six Strategic Committees

      July 8, 2026

      Not only NSC, EFCC should investigates NFF, other federations too

      June 5, 2026
    • Analysis

      Kano Sports: Huge expectations for new Kano Pillars, Sports Commission Boards

      June 29, 2026

      Kano Pillars’ survival hopes alive despite tough battle ahead

      May 22, 2026

      NPFL survival at stake: Relegation battle heads into final day

      May 14, 2026

      Kano Pillars: Final words before crucial Plateau United FC encounter

      May 12, 2026

      Alleged Bias in Kano Sports Support: What Kano FA Should Address

      May 5, 2026
    • Personality Profiles

      Engr. Aikawa assumes Office as pioneer Deputy Rector (Academics)

      July 6, 2026

      Making of a Leader: Dr. Garba A. Adamu’s journey from laboratory to leadership

      July 4, 2026

      AbdulGaffar I. Dawakin Tofa: Shaping public discourse through journalism, broadcasting

      June 24, 2026

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Gasar Kofin murnar cika shekara biyun Gwamna Abba: Mai Samba yayi hamdala
    Sports News

    Gasar Kofin murnar cika shekara biyun Gwamna Abba: Mai Samba yayi hamdala

    Sani YusifBy Sani YusifJuly 28, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    8

    Ba wani mahaluki a jahar Kano musamman a karamar hukumar Dala da zaifi Ali Nayara Mai Samba murna jiya Lahadi a lokacin da ya tara dubunnan matasa na cikin birni da kewaye a filin wasa na Kurna Babban Layi a wajen wasan karshe na Mai Samba Unity Cup 2025.

    Ganin dandazon jamaar da suka taro a wajen wasanne yasa Mai Samba cikin farin ciki, da annashuwa  wanda kuma ya sashi kasa zaune da kuma tsaye sai dai zirga zirga.

    Hakika taro yayi taro domin Ali Nayara Mai Samba yayi kira kuma matasa sun amsa don ta ko’ina tuttudowa sukeyi duk da haduwar hadari, al’amarin da ya tsunduma Mai Samba cikin murna da faraa tun kafin a fara wasan har zuwa kammala shi.

    Kasar wadda kungiyoyin kwallon kafa na ungowowi 28 suka shiga an shirya tane don ta ya maigirma gwamna Abba Kabir Yusuf murnar cika shekaru biyu akan karagar mulkin Kano da kuma ayyukan raya jiha da yake ta aiwatarwa.

    Kungiyoyin unguwa ishirin da takwas din da suka fafata a kasar sun hada da Kurna. A,

    Hotoro, Gwale, Gwammaja, Kawo, Kwankwaso, Tsakuwa , Kurna. C, Kofar Ruwa , Kofar Mata, K/Wai-Dwn, Bichi da kuma Miltara.

    Sauran sun hada da Sabon Gari, Fagge, K/Nasarawa, Dorayi, Rijiyar Lemo. B, Alfindiki, Dala, Yakasai, Brighet, Gwammaja.B, Rijiyar Lemo. A, Bachirawa, Kurna. B, Goron Dutse da kuma Bakin Kasuwa.

    A wasan karshen dai kungiyar unguwar Kurna C ce ta lallasa kungiyar unguwar Brighet da ci biyu da daya. A wasan neman na uku kuma kungiyar unguwar Mil Tara ce ta doke kungiyar  Kurna. A da ci daya mai ban haushi.

    A karshen wasan a bada lambobin yabo wanda aka fara bawa Mai Girma Gwamna Alh. Abba Kabir Yusuf

    Wanda an mikawa wakilin Gwamnan lambar yabonne don ayyuka tukuru da kuma kokarinsa na wanzan da zaman lafiya da kuma hana shaye shaye da kwacen waya da kuma ciyarda wasannin gaba a jihar Kano.

    Mutum na biyu da aka karrama da lambar yabo shine Hon. Mustapha Rabi’u Musa Kwankwaso, kwamishinan matasa da wasanni na jihar Kano. Wanda aka karramashi don kokarinsa na bunkasa matasa da kuma wasanni a ko’ina cikin yankin jihar nan.

    Ogan boye, shugaban karamar hukumar Nasarawa ma an karramashi saboda zama shugaba na gari don nasarorin da yake samu a mulkinsa da kuma ci gaban matasan Kwankwasiyya.

    Suraj Imam, shugaban karamar hukumar Dala ma an karramashi da lambar iya kyakkyawan shugabanci da kuma kokarinsa na cigabn jamaar karamar hukumar Dala.

    Haka kuma an karrama Sani Danja don kokarinsa na cigaban matasa a jihar Kano.

    Sabon Janaral Manaja na kungiyar Kano Pillars ma watau Ahmed Musa (M.O.N) an karramashi da lambar kokari wajen cigaban al’umma musamman a bangaren wasanni da kuma tallafawa gajiyayyu.

    Dan wasa Rabiu Ali Fagge ma an karramashi don zama fitatcen dan wasa a gasar Nayara Sallah Competition da kuma kokarinsa a wasan premier ta kasa.

    Haka kuma  Shehu Abdullahi ma ya karbi lambar yabo wajen kokarinsa na koyawa matasa wasa da kuma yin aiki tukuru.

    An kuma raba kyaututtuka ga yan wasan da sukayi shura a garsar wanda Auwal Ali Malan dan wasan Kurna A wanda yafi kowa jefa kwallaye a raga ya lashe da cin kwallo shida.

    Naziru Auwalu dan wasan kungiyar  Kurna C da Ladan Muhd na kungiyar Tsakuwa sune suka lashe kyautar kwararrun yan wasan gasar watau Best young players of the tournament.

    Haka kuma dan wasa Muhd Ahmad na kungiyar Miltara ne mai tsaron gidan da yayi fice a gasar watau Best Goalkeeper.

    Fahad Usman na kungiyar Brighet ne ya lashe kyautar dan wasan da yafi tausayi watau Fair play player of the tournament.

    Sani Zidan na kungiyar Miltara shine ya zama kocin da yafi fice watau Best Coach of the tournament.

    Kungiyar Brighet it ace ta zama kungiyar da tafi kowacce watau Best Team. Su kuma kungiyar Hotoro sune suka zama wadanda sukafi kowa da’a watau Most discipline Team.

    Da yake magana da wannan kafa, Ali Nayara Mai Samba wanda kuma shine shugaban kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ya bayyana godiyarsa ga dimbin jamaar da suka halarci wajen waccan gasar da kuma musu fatan alheri.

    Ya kuma sheda mana cewa ya yanke shawarar shirya gasarne don ta ya mai girma Gwamna Abba Kabir Yusuf murnar cika shekaru biyu akan garagar mulkin jihar Kano.

    Mai Samba ya kuma godewa mai girma gwamna saboda irin ayyukan alheri da yake ta aiwatarwa a fadin yakin jihar Kano.

    Ya kuma yi adduar kara samun nasarori akan wadanda ake samu.

    cin kofin Gasar ta ya gwamba Abba
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleOgun State’s Sports Development: My exact dream for Kano’s sports
    Next Article After unprecedented 2 year in office: Mai Samba assembles samba artists for Gov Abba
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

    July 14, 2026

    New Kano Pillars Management: Any hope for real change?

    July 13, 2026

    Gombe Emir’s Cup: Organisers unveil quarter-final fixtures, match dates

    July 10, 2026

    Gombe Emir’s Cup Quarter-Finals set as Eight Clubs progress

    July 8, 2026

    Babangida takes helm of Kano State Sports Commission

    July 6, 2026

    Sports sector reforms: National Sports Commission earns ABU’s praise

    July 6, 2026
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Katsina Government seeks Kano’s expertise to establish Culture, Reorientation Agency

    July 15, 2026

    NTDA partners Ringo Sport Club for NISPRISPORT 2026

    July 15, 2026

    NASTOCE 2026: Chief Abiodun Odusanwo, Dr. Badaki Aliyu Earn Meritorious Honours

    July 14, 2026

    NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

    July 14, 2026

    New Kano Pillars Management: Any hope for real change?

    July 13, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.