Hakika mutane da dama sun yi hasashen cewa kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars za ta kasance cikin sahun gaba wajen daukar sababbi da zakakuran ’yan wasa bayan da Hukumar Gudanar da Gasar Firimiya ta Kasa ta bada damar hakan.
Kungiyoyi da dama kamar Barau FC, Wikki Tourists, Kwara United da sauran su sun yi amfani da wannan dama wajen ceto kwararrun ’yan wasa daga wasu kungiyoyi domin karfafa nasu bangaren gasa.
Sai dai abin mamaki, har zuwa rufe wannan damar, Kano Pillars ba ta samu sababbin ’yan wasa fiye da biyu ba, duk da kowa ya san kungiyar na matukar bukatar karin karfi, ganin yadda take fama da rashin kwazo a wannan kakar wasa.
Wannan lamari ya haifar da cece-kuce daga masana wasanni, masu sharhi, magoya baya da ma wasu daga cikin kungiyar magoya bayan Kano Pillars.
Sai dai tambayar da ke yawo a zukatan jama’a ita ce: me ya sa shugabannin Kano Pillars suka bari wannan muhimmiyar dama ta wuce su, alhali sun fi kowa sanin halin da kungiyarsu ke ciki?
Shin sun mika bukatarsu ga gwamnati domin amincewa da daukar karin ’yan wasa amma aka yi shiru? Ko kuwa sun gamsu da kokarin ’yan wasansu ne? Ko kuma akwai wani dalili da ya fi karfinsu da ya hana hakan faruwa?
Sai bayan samun amsoshin wadannan tambayoyi ne za a fahimci hakikanin dalilin da ya sa mahukuntan kungiyar suka kasa yin katabus, duk da sanin matsalolin da kungiyar ke fuskanta.
Da yawancinmu muna da sanin cewar ba kamar kungiyar Barau ko kungiyoyi na mutum daya ba, yanke hukunci a kungiyar gwamnati nada wahalar gaske sanin biye-biyen da zaayi kafin a sahale ayi abun.
Ko da yake har yanzu babu cikakken bayani a hukumance, wannan kafar za ta ci gaba da bin diddigi domin gano gaskiyar lamarin.
Bugu da kari, a kakar zabe muke wanda da gwamnati da jigajiganta ba wannan abin bane a gabansu. Balantana wananan lokacin da gwamna ya sauya sheka zuwa wata jam’iyya.
Ku kasance tare da mu.
