Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Barau FC under pressure to investigate alleged GM misconduct

      March 10, 2026

      FIFA Coach Educator Pass way Course: Kano’s Gwadabe in Rwanda

      March 5, 2026

      Pillars’ triumph over El-Kanemi: Mai Samba elated after commanding win

      February 23, 2026

      Abuja NASTOCE ’26: 12 Ministries, 64 Agencies, 36 States set to participate

      February 20, 2026

      Yohanna wins LGAN inaugural kitty; Ahmed targets Continental Glory

      February 18, 2026
    • Column

      NFF’s Gusau: Balancing progress with persistent challenges

      March 9, 2026

      Undue advantages enjoyed by CAF-participating clubs in NPFL

      March 2, 2026

      From Duty to Pitch: Kano SWAN honours NDLEA’s Sports-Driven Jamilu U. Adamu

      February 23, 2026

      Pandemonium: As NPFL matches turn into War Zones

      February 16, 2026

      NPFL Under Fire: Governance, sanctions with fight for transparency

      February 9, 2026
    • News & Media

      International Women’s Day: Women in Hospitality, Tourism celebrate excellence, professionalism

      February 22, 2026

      Kano Football Coaches host Modern Coaching Seminar for members

      January 7, 2026

      Oseni replaces Ramat as NERC chairman after Senate rejection

      December 19, 2025

      Ahned Musa: Honoring 15 Years of Dedication and Selfless Service

      December 17, 2025

      2025 CIPPON Annual General Meeting (AGM) to Hold in Kano

      November 22, 2025
    • Analysis

      Memo to KNSG’s committee on Kano Pillars’ performance

      February 9, 2026

      Re-Calls on Gov. Yusuf to Dissolve Kano Pillars Board, but retain GM Musa

      February 6, 2026

      Kano Pillars and Sports Commission: Story of Dwindling Fortunes

      February 5, 2026

      Jan kafar Pillars wajen ɗaukar sababbin ’yan wasa: Me ke faruwa?

      February 4, 2026

      Gaskiyar banbanci tsakanin Kano Pillars da Barau FC

      February 4, 2026
    • Personality Profiles

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Hana yan tawagar wasannin nakasassu hakkinsu: A ina aka kwana ne?
    Sports News

    Hana yan tawagar wasannin nakasassu hakkinsu: A ina aka kwana ne?

    Sani YusifBy Sani YusifMarch 18, 2024
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram

    Yau  wata uku cif da zuwa da dawowar yan wasan jihar Kano daga wasan kasa na nakasassu watau (2023 National Para-Games Competition) wanda akayi a Abuja amma har yanzu hukumar wasanni ta jihar Kano (Kano State Sports Commission) bata biya mafi yawancin yan tawagar zuwa Abujan hakkokinsu ba (Daily Travelling Allowances).

    Wani abin haushi datakaici wanda kuma ya zubarwa da hukumar wasannin ta jihar Kano mutunci a idon jamaa shine kasa wani katabus don karbowa mafi yawancin yan tawagar hakkokinsu daga gwamnati kamar yadda suke cewa.

    Bincike ya nuna mummunar wahalar da dukkannin yan tawagar jihar Kano suka sha a lokacin da suke Abuja gabadayansu saboda rashin biyansu alawus din da yakamata a basu tun kamin tafiyar tasu zuwa babban birnin tarayyar Nijeriya, Abuja.

    Idan bamu manta ba, hukumar wasan ta jihar Kano ta tura yan wasa, masu horar dasu, sakatarorin tsare-tsare, likitoci, yan jarida, direbobi, jami’en tsaro da sauransu zuwa Abuja ba tare da basu kudaden alawus dinsu ba (DTA) da alkawarin damka musu kudadensu da sun isa Abuja.

    Amma wani abin takaici da suka isa Abuja sai hukumar wasannin tayi musu kememe al’amarin da ya jefa dukkannin yan tawagar cikin rudani da dimuwa saboda tsanani rashin kudi da suka shiga.

    Wannan ya faru ne saboda mafi yawancinsu basu da kudin cin abinci balantana na inda zasu kwanta ga shi kuma basusan kowa a Abuja ba. Ga kuma rashin kudin sufuri daga can zuwa can.

    Da wuya tayi wuya sai suka koka ta hanyar yan jaridun da suke tare dasu wanda yasa mukaddashin hukumar wassannin ta jihar Kano, Malam Bala Malam magantuwa.

    A jawabinsa ga yan jarida Malam Bala ya bayyana karbar Naira miliyan tara (N9m) cikin miliyan 30 da suka nema daga gwamnati wanda kuma a cewarsa yayi amfani da kudin ya biya kudin rijistar yar wasa al’amarin ya rudarda jama’a da dama.

    A wancen lokacinne Malam Bala yayi alkawarin biyan kowa alawus dinsa da zarar sun komo gida jihar Kano.

    Bincike ya nuna mafiyawancin yan tawagar mutanene masu iyali kuma sun bar gida da alkawarin da sun isa Abuja zasu turowa iyalensu kudin kashewa wanda rashin biyan ya jefasu cikin wata dimuwar.

    Wani  abin haushi kuma shine da suka komo gida alkawarin bai cika ba domin mukaddashin shugaban hukumar yayi biris da maganar, al’amarin da yasa yan tawagar kara magantuwa ta kafafaen yada labarai masu dama.

    Wannance ta firgita shi inda yaje ya samo kudi amma kash a maimakon ya biya dukkannin yan tawagar sai ya zabi wasu a cikinsu har da yan jarida ya biya ya kuma manta da sauran. Al’amarin da jama’a da dama sukayi Allah wadai da kuma kokarin toshe bakin masu magana wanda yayi nasara.

    Wani karin abin takaicin kuma shine cikin mutanen da Malam Bala yaki biya akwai likitoci da dirobobi wadanda arosu akayi daga wasu ma’aikatu don su taimaka a sami nasarar tafiyar.

    Bugu ga kari  su kuma sauran kamarsu sakatarori su suke samo masu horarwa sannan su kuma masu horarwa su samo yan wasa.

    Amma ya biya yan wasa ya manta da sakatarori da masu horarda yan wasan wanda shima babban koma bayane.

    A ganina biyan wasu yan wasa da kuma kin biyan wadancen jami’en ba daidai bane kuma ya nuna rashin sanin aiki da kuma rashin iya gudanarwa.

    A nan nake tunawa Malam Bala yadda ya karbo naira miliyan tara ta farko daga cikin miliyan talatin da gwamnati ta amince a kasha da kuma kudin ya kara  amsowa wadanda bamusan yawansu ba ya biya wasu yan wasa da yan jarida, yakamata ya yi namijin kokari wajen nemo sauran kudaden ya biya masu hakki hakkinsu.

    Yakamata Malam Bala ya sani cewa shi shugabanci ba zama ko iya zama a ofis bane. Yin abin da yakamata a lokacin da yakamata shine shugabanci.

    Yin shiru ba gwaninta bane domin a watan goma sha daya za a sake wani wasan, da wane ido ko fuska zaa kara neman wadannan mutanen don samun gudummawarsu?

    Bugu da kari, shugaban hukumar wassannin yakamata ya  sani cewa da wadannan mutanen da bayaganin kimarsu da mutuncinsu basu agazaba, da tafiyar zuwa Abuja bata yiwu ba

    Tun da har mai girma gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf ya amince a biya banga dalilin da Malam Bala zai rinka baya-baya ba. Ya tashi ya je inda ya kamata don karbowa mutane hakkinsu.

    Ya kuma kamata Malam Bala ya fara amfani da kudaden shiga da hukumarsa take samu daga sitadia ta Sabon Gari da ta Kofar Mata da kuma filin wasa na Ado Bayero Squre don fara rage kudin kafin ya amso wadancan.

    Hakkinsu Hana yan tawagar wasanni
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleJamaa, asa Kano Pillars cikin addua
    Next Article Pain and gain of a writer
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Barau FC under pressure to investigate alleged GM misconduct

    March 10, 2026

    FIFA Coach Educator Pass way Course: Kano’s Gwadabe in Rwanda

    March 5, 2026

    Pillars’ triumph over El-Kanemi: Mai Samba elated after commanding win

    February 23, 2026

    Abuja NASTOCE ’26: 12 Ministries, 64 Agencies, 36 States set to participate

    February 20, 2026

    Yohanna wins LGAN inaugural kitty; Ahmed targets Continental Glory

    February 18, 2026

    Inferno: Mai Samba mourn Singer Market fire victim

    February 16, 2026
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Barau FC under pressure to investigate alleged GM misconduct

    March 10, 2026

    NFF’s Gusau: Balancing progress with persistent challenges

    March 9, 2026

    FIFA Coach Educator Pass way Course: Kano’s Gwadabe in Rwanda

    March 5, 2026

    Undue advantages enjoyed by CAF-participating clubs in NPFL

    March 2, 2026

    Pillars’ triumph over El-Kanemi: Mai Samba elated after commanding win

    February 23, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.