Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      FIFA Coach Educator Pass way Course: Kano’s Gwadabe in Rwanda

      March 5, 2026

      Pillars’ triumph over El-Kanemi: Mai Samba elated after commanding win

      February 23, 2026

      Abuja NASTOCE ’26: 12 Ministries, 64 Agencies, 36 States set to participate

      February 20, 2026

      Yohanna wins LGAN inaugural kitty; Ahmed targets Continental Glory

      February 18, 2026

      Inferno: Mai Samba mourn Singer Market fire victim

      February 16, 2026
    • Column

      NFF’s Gusau: Balancing progress with persistent challenges

      March 9, 2026

      Undue advantages enjoyed by CAF-participating clubs in NPFL

      March 2, 2026

      From Duty to Pitch: Kano SWAN honours NDLEA’s Sports-Driven Jamilu U. Adamu

      February 23, 2026

      Pandemonium: As NPFL matches turn into War Zones

      February 16, 2026

      NPFL Under Fire: Governance, sanctions with fight for transparency

      February 9, 2026
    • News & Media

      International Women’s Day: Women in Hospitality, Tourism celebrate excellence, professionalism

      February 22, 2026

      Kano Football Coaches host Modern Coaching Seminar for members

      January 7, 2026

      Oseni replaces Ramat as NERC chairman after Senate rejection

      December 19, 2025

      Ahned Musa: Honoring 15 Years of Dedication and Selfless Service

      December 17, 2025

      2025 CIPPON Annual General Meeting (AGM) to Hold in Kano

      November 22, 2025
    • Analysis

      Memo to KNSG’s committee on Kano Pillars’ performance

      February 9, 2026

      Re-Calls on Gov. Yusuf to Dissolve Kano Pillars Board, but retain GM Musa

      February 6, 2026

      Kano Pillars and Sports Commission: Story of Dwindling Fortunes

      February 5, 2026

      Jan kafar Pillars wajen ɗaukar sababbin ’yan wasa: Me ke faruwa?

      February 4, 2026

      Gaskiyar banbanci tsakanin Kano Pillars da Barau FC

      February 4, 2026
    • Personality Profiles

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Hajia Ain Jafaru Fagge: Kifi na ganinka mai jar koma
    Sports News

    Hajia Ain Jafaru Fagge: Kifi na ganinka mai jar koma

    Sani YusifBy Sani YusifMay 21, 2024
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram

    Idan mai karatu mai bibiyar kafofin sadarwa na yanar gizo ne zai iya yin kicibis ko kuma samun labarin kiran da wata hajiya a jihar Kano keyi na kira da rokon mai girma gwamnan jihar Kano injniya Abba Kabir Yusuf da ya tashi filin wasa na Sani Abacha dake Kofar Mata daga inda yake.

    Hajiyar mai suna Ain Jafaru Fagge wanda kowa yasanta a  matsayinta na sananniyar yar siyace ta bada dalilan kiran da korafin nata ga mai girma gwamna saboda abubuwan da suka biyo bayan kafa filin wasan tun lokacin da aka kafa shi har izuwa yau.

    A cewar ta, kasancewar  filin wasan na Kofar Mata a wajen da yake na cutarda mutane da yawa musamman na asibitin Murtala don ana firgita marasa lafiya da akeyi duk lokacin da aka kamala wasa a filin.

    Hajiyar ta kara da cewar  ana cutar kuma da mutanen Kofar Mata wajen shigar musu gida da makamai da akeyi, tare da mutanen Koki da mutanen Fagge.

    Hajiyar ta kuma kara da cewa har yan kasuwar Singa, Wapa da na kwari dana Sabon Gari duk na cutuwa da illar da abinda ke faruwa a duk lokacin da akayi wasa a filin wasa na Kofar Mata.

    Ta bada shawarar fidda filin wasan na Kofar Mata wajen gari domin a ganinta nanne yafi dacewa da shi.

    Amma wani abu da hajiyar ta manta ko ta kasa ganewa shine, suwaye masu aikata barnar? kuma su waye suke daure musu gindin yin barnan? Ko kuma su waye iyayen gidan su?

    Sufa wadannan masu aikata wannaan danyen aikin da Hajiya Ain Jafara take ta kwakwazo ba wasu bane illa yaransu ne. Kuma su suke daure musu gindin yin abinda sukeyi. Su suke sawa ana sakinsu domin yaransune.

    Ya kamata Hajiya ta sani cewa kowa ya san inda ta nufa da korafinta. Ba dan Allah tayi korafin ba. In ina ganin turo ta akayi.

    A ganina so kawai ake a sami kafar rushe filin wasan da aka kashe makudan kudin kasarnan wajen ginawa don ita da irinta su sami kasonsu na mallakar filayen gina shaguna.

    Wani abin da Hajiya ta kara mantaewa shine, a fadin jiharnan kaf dinta ba masu taimakawa lalacewar matasanmu irinsu yan siyasa. Domin yan siyasa ke daure musu gindin yin munanen ayyukan da sukeyi.

    Na duba kaf fadin jiharnan ban ga inda wani malami ko dan kasuwa ko basarake ke ajiye ko tafiya da yan daba da shaye-shaye ba.

    Yan siyasane kawai ke lalatasu kuma su suke amfanarsu gashi kuma abin kunya tana  kukawa da dasu.

    Duk masu irin wannan mummunar bukata don kawai sunason a mallaka musu filin gina shaguna idan an rushe filin wasan bazasu sami nasara ba. Domin miliyoyin masu ruwa da tsaki na harkar wasanni baza su barsu ba.

    Cewar a wasu kasashe filayen wasa a wajen gari suke, ba daidai bane  domin idan ta duba filinye wasanni na kasashen turai duk a cikin jama suke baa gefen gari ba.

    Na dauka Hajiya yanzu zatayi kira ga mai girma gwamana ya duba mummunan halin da makarantun firamaren yayan talakwwa suke.

    A halin yanzu ba wata firamare da dan talaka ke zuwa wadda ke da abin zama balantana na rubutu.

    Ko kuma me yasa Hajiya bazatayi kira ga mai girma gwamna da yasamawa yaran abinyi ba?

    Kifi na ganinka mai jar koma.

    Hajia
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleRevitalization of Kano sports: Engr Yusuf urges to appoint Rabiu, Maizare to head Kano State Sports Commission
    Next Article Federation Cup victory: Little commends players…thanks commissioner Mustapha, Gov Abba
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    FIFA Coach Educator Pass way Course: Kano’s Gwadabe in Rwanda

    March 5, 2026

    Pillars’ triumph over El-Kanemi: Mai Samba elated after commanding win

    February 23, 2026

    Abuja NASTOCE ’26: 12 Ministries, 64 Agencies, 36 States set to participate

    February 20, 2026

    Yohanna wins LGAN inaugural kitty; Ahmed targets Continental Glory

    February 18, 2026

    Inferno: Mai Samba mourn Singer Market fire victim

    February 16, 2026

    Nigeria’s Sports Tourism takes center stage …as NASTOCE 2026 launches in Abuja

    February 8, 2026
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    NFF’s Gusau: Balancing progress with persistent challenges

    March 9, 2026

    FIFA Coach Educator Pass way Course: Kano’s Gwadabe in Rwanda

    March 5, 2026

    Undue advantages enjoyed by CAF-participating clubs in NPFL

    March 2, 2026

    Pillars’ triumph over El-Kanemi: Mai Samba elated after commanding win

    February 23, 2026

    From Duty to Pitch: Kano SWAN honours NDLEA’s Sports-Driven Jamilu U. Adamu

    February 23, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.