Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Musa Commends Nestlé Milo for sports clinics, rallies sponsors for school sports

      August 15, 2026

      Falgore presents appointment letter to Ahmad Suraj

      August 13, 2026

      2026 KASHIGA Staff Games: Planning, preparations commence

      August 13, 2026

      Hard work pays off as Jamilu Uba earns double appointment in Kano Sports

      August 11, 2026

      Babangida formally assumes duty as Kano State Sports Commission Chairman, receives Appointment Letter

      August 11, 2026
    • Column

      Gov Abba 3rd Year Anniversary Cup: Mai Samba overjoyed, calls for more inclusive government

      August 14, 2026

      23rd NSF: Why limiting games to 20 Sports raises serious questions

      August 7, 2026

      Is Kano Pillars following Barau FC’s lackadaisical approach to players recruitment?

      July 31, 2026

      Has Barau FC management lost sight of Senator Barau’s vision?

      July 24, 2026

      Free transfer blow: Should Kano Pillars have let Fabian Nworie leave for nothing?

      July 17, 2026
    • News & Media

      NAN Chief, Ali M. Ali honoured by NASTOCE, reaffirms support for NISPRISPORT 2026

      July 29, 2026

      NTT Summit 2026: Tourism minister advances one-government policy to power skills revolution, 4 Million Jobs

      July 28, 2026

      Keyamo, Musawa confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

      July 24, 2026

      Keyamo, Musawa Confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

      July 24, 2026

      Katsina Government seeks Kano’s expertise to establish Culture, Reorientation Agency

      July 15, 2026
    • Analysis

      Kano Sports: Huge expectations for new Kano Pillars, Sports Commission Boards

      June 29, 2026

      Kano Pillars’ survival hopes alive despite tough battle ahead

      May 22, 2026

      NPFL survival at stake: Relegation battle heads into final day

      May 14, 2026

      Kano Pillars: Final words before crucial Plateau United FC encounter

      May 12, 2026

      Alleged Bias in Kano Sports Support: What Kano FA Should Address

      May 5, 2026
    • Personality Profiles

      Engr. Aikawa assumes Office as pioneer Deputy Rector (Academics)

      July 6, 2026

      Making of a Leader: Dr. Garba A. Adamu’s journey from laboratory to leadership

      July 4, 2026

      AbdulGaffar I. Dawakin Tofa: Shaping public discourse through journalism, broadcasting

      June 24, 2026

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Kwanaki darin Hajiya Hauwa Isa Ibrahim na jagorancin ARTV
    News & Media

    Kwanaki darin Hajiya Hauwa Isa Ibrahim na jagorancin ARTV

    Sani YusifBy Sani YusifSeptember 10, 2024
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram

    A makon da ya gabatane watau ranar 6 ga watan Satumbar wannanshekarar ta 2024 , mai rikon mikamin shugabancin Gidan Talabijin na Abubakar Rimi(ARTV), Hajiya Hauwa Isa Ibrahim ta cika kwana dari cif da darewa kan mulkin gidan talabijin din.

    Zamanta mai rikon mikamin shugabancin gidan watau (Acting Managing Director)  Abubakar Rimi Television (ARTV) ke wuya, Hajiya Hauwa ta farfado da gidan daga dogon suman da yayi saboda rashin kulawa da kuma sassaita ayyukan gidan talabijin din ta hanyar bada  shugabanci nagari wanda ya sami rauni daga shugabannin da suka shude.

    Babu shakka kwana darin da Hajiya Hauwa tayi tana jagorancin ARTV, kwanaki ne masu tarin albarka saboda darurruwan cigaban da ta kawu gidan talabijin din wanda a lokutan baya ake kira CTV 67.

    Kasancewarta shugabar ARTV keda wuya, Hajiya Hauwa ta fara saitawa maaikatan gidan alkibla don su rinka zuwa aiki da kuma tashi akan lokaci.

    Nan take ta dakatarda zuwa aiki a makare da kuma fashin zuwa aiki wanda a lokutan baya yasha kan gidan.

    Tunda masu iya magana suna cewa, daga na gaba ake  ganin zurfin ruwa, Hajia Hauwa ta fara nuna kyakkyawan misali wanda yasa ita ke fara zuwa aiki kullum don nunawa sauran maaikatta abinda ya kamacesu.

    Jagoriyar ta  gyara dangantakar shugabancin gidan da dukkannin ma’aikata wanda shine musabbabin samun dinbin nasarorin da ta samu a wadannan kwanaki dari masu tarin albarka. Saboda kowane maaikaci a halin yanzu na aiki tukuru da kuma kula da kuma bin nagabansa.

    Sanin mahimmancin ma’aikatane yasa  Hajiya Hauwa daukar hakkokinsu da muhimmancin gaske wanda yasa ta sasu a gaba da kuma gabatar dasu a duk lokacin da aka kawo mata gabanta.

    Haka kuma shugabancinta ya samawa gidan sababbin  kayayyakin aiki na zamani a kusan kowane bangare da suke bukatarsu don inganta ayyukan ma’aikatan.

    Hakan yasa daukacin maaikatan gidan talabijin din ARTV tashi tsaye da kuma daukar aikinsu da mahimmanci ba dare ba rana wanda ya kyautata sauti da kuma hotunan da talabijindin take yadawa.

    Wani abu daya da Hajiya Hauwa Isa Ibrahim shine, macece mai haba-haba da kowa da kowa  amma bai hanata tsawatawa ba domin batason wasa da aiki.

    Saboda tabbatar da cewa ayyuka na tafiya daidai,  Hajiya Hauwa ta aiwatar da gyare-gyare a dakunan dakunan  yada labarai na gidan (Studio) da kuma samarda na’urorin daukar hotona da kuma komputoci na kan tebur (Desktop) da na kuma kan cinya (Laptop) duk don samun saukin aikin maaikatan gidan.

    Hajiyar ta kuma samarda manya-manyan abubuwan saukewa da kuma ajeye labarai, hotuna da kuma fina-finai don amfani dasu nan take ko kuma nan gaba.

    Ta samarda sabuwar na’urar wuta (transformer) da kuma gyara injin bada wuta na wucin gadi don samun wutar lantarki akowane lokaci.

    Bakamar da ba, Hajiya Hauwa tayi nasarar mayar da shirye-shiryen gidan talabijin din ARTV awa ishirin da hudu ba dare ba rana, al’amarin da yasa gidan  samun karin masu kallo a fadin duniya bakai daya. Abinda yasa Hajiya Hauwa zama shugabar gidan ta farko da ta ciri tuta da samun yabo ta ko’ina a fadin yakin jiharnan da kuma duniya baki daya.

    Hajiyar wadda mafi yawan mutane ke mata kirarin “Mace mai kamar maza” saboda kokarinta da kuma aikitukurunta ta kuma sami nasarar dora shirye-shiryen gidan ARTV din kan Tauraruwar NIGCOM SAT abinda yasa ganin shirye-shiryen gidan ARTV din a dukkannin fadin duniya.

    Hajiya Hauwa ta kuma zamanantar da shirye-shiryen gidan talabijin na ARTV ta kuma yada ayyukansa kan kafofin sadarwa na Twitter, Instagram, Facebook, da kuma TikTok, al’amarin daya karawa gidan masu kallo, saurare da kuma karanttawa a fadin duniya baki daya.

    A halin yanzu Hajiya Hauwa ta kuma maida ARTV kafa ta farko wajen nunawa da kuma tallata dariruwan ayyakan alheri da mai girma Gwamnan jihar Kano, Injiya Abba Kabir yaketa aikatawa a fadin jihar Kano.

    Wannanne yasa a lokacin da mai girma gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf ya kai ziyarar gani da ido kwanan baya, gwamannya yaba mata sosai saboda ganin ayyukan da ta aiwatar da kudaden   da ya sahale mata don gyara gida ARTV din.

    A dukkannin bangarorin daya ziyarta, gwamna sai murmushi yake tayi saboda gamsuwa da abubuwan da yaganewa idanunsa.

    Don haka jamaa da dama ke adduar cigaba, nasara da kuma daukaka ga Hajiya Hauwa a dukkannin ayyukanta da kuma inda ta sami kanta yanzu da kuma nan gaba.

    Haka kuma, soyayya da kuma kaunar gwamna yasa ta daukar nauyin gabatar da bikin wasan gasar kwallon kafa ta kananan hukumomi 44 na jihar Kano saboda murnar cikarsa shekara daya a bisa mukin Kano.

    A karshe dole a godewa mai girma gwamna wajen zakulo ita Hajiya Hauwa Isa Ibrahim da kuma dora ta kan wannan mukamin. Ga kuma bata hadinkai a inda yake amincewa da dukkannin abubuwa da ta kawo gabansa.

    Fatanmu shine mai girma gwamna ya tabbatar mata da mikaminnata don samun natsuwar da cigaba da inganta ayyukan ARTV da kuma tallata da kuma yada ayyukan mai girma gwamna.

    ARTV jagorancin Kwanaki dari
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleKano Pillars Media directorate: Good initiative, but…
    Next Article Celebrating 100 Days of sports loving Acting ARTV MD, Hajiya Hauwa Isa Ibrahim
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    NAN Chief, Ali M. Ali honoured by NASTOCE, reaffirms support for NISPRISPORT 2026

    July 29, 2026

    NTT Summit 2026: Tourism minister advances one-government policy to power skills revolution, 4 Million Jobs

    July 28, 2026

    Keyamo, Musawa confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

    July 24, 2026

    Keyamo, Musawa Confirmed as speakers for 9th National Tourism Transportation Summit & Expo 2026

    July 24, 2026

    Katsina Government seeks Kano’s expertise to establish Culture, Reorientation Agency

    July 15, 2026

    NTDA partners Ringo Sport Club for NISPRISPORT 2026

    July 15, 2026
    View 1 Comment

    1 Comment

    1. Zahraddeen zakari on September 10, 2024 2:54 pm

      Masha Allah

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Musa Commends Nestlé Milo for sports clinics, rallies sponsors for school sports

    August 15, 2026

    Gov Abba 3rd Year Anniversary Cup: Mai Samba overjoyed, calls for more inclusive government

    August 14, 2026

    Falgore presents appointment letter to Ahmad Suraj

    August 13, 2026

    2026 KASHIGA Staff Games: Planning, preparations commence

    August 13, 2026

    Hard work pays off as Jamilu Uba earns double appointment in Kano Sports

    August 11, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.