Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

      July 14, 2026

      New Kano Pillars Management: Any hope for real change?

      July 13, 2026

      Gombe Emir’s Cup: Organisers unveil quarter-final fixtures, match dates

      July 10, 2026

      Gombe Emir’s Cup Quarter-Finals set as Eight Clubs progress

      July 8, 2026

      Babangida takes helm of Kano State Sports Commission

      July 6, 2026
    • Column

      With full government support, Babangida, Maizare, others must produce results

      July 10, 2026

      Gov. Abba’s listening approach: Key to reviving Kano Pillars, Kano Sports Commission

      July 3, 2026

      Kano State Sports under siege: Governor Abba must hear it

      June 26, 2026

      Madrid, Barcelona Supporters’ friendly meeting in Kano: A welcome initiative, but…

      June 19, 2026

      2026 World Cup Qualifiers: Where I disagree with Gara-Gombe’s position

      June 12, 2026
    • News & Media

      NASTOCE 2026: Chief Abiodun Odusanwo, Dr. Badaki Aliyu Earn Meritorious Honours

      July 14, 2026

      To Reposition Broadcasting in Nigeria: BON constitutes Six Strategic Committees

      July 8, 2026

      Not only NSC, EFCC should investigates NFF, other federations too

      June 5, 2026

      Dr. Maizare elected Vice President, Marathon Organizers Forum

      May 19, 2026

      Sports as Reform: As Kano NDLEA takes Anti-Drug Campaign to Goron Dutse Centre

      April 28, 2026
    • Analysis

      Kano Sports: Huge expectations for new Kano Pillars, Sports Commission Boards

      June 29, 2026

      Kano Pillars’ survival hopes alive despite tough battle ahead

      May 22, 2026

      NPFL survival at stake: Relegation battle heads into final day

      May 14, 2026

      Kano Pillars: Final words before crucial Plateau United FC encounter

      May 12, 2026

      Alleged Bias in Kano Sports Support: What Kano FA Should Address

      May 5, 2026
    • Personality Profiles

      Engr. Aikawa assumes Office as pioneer Deputy Rector (Academics)

      July 6, 2026

      Making of a Leader: Dr. Garba A. Adamu’s journey from laboratory to leadership

      July 4, 2026

      AbdulGaffar I. Dawakin Tofa: Shaping public discourse through journalism, broadcasting

      June 24, 2026

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Rashin kokarin Kano Pillars da Barau: Sai fa gwamnati ta yi wani abu
    Sports Analysis

    Rashin kokarin Kano Pillars da Barau: Sai fa gwamnati ta yi wani abu

    Sani YusifBy Sani YusifOctober 7, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    1aa

    Hakika gwamnati a cikin rayuwa da harkokin jama’arta yar kallo ce. Sai da babban aikinta shine sa ido da kuma samar da tsarirrika da yanayi wanda jama’arta zasu sami damar tafiyar da harkokinsu a sauwake cikin lumana.

    Gwamnatoci na samun kwanciyar hankali da kuma gudanar da mulkinsu a saukake, idan sun fuskanci jama’arsu na da abinyi kuma harkokinsu na wanzuwa ko tafiya daidai ba cuta ba kuma cutarwa.

    Kowa ya sani ba aikin gwamnati bani shiga harkokin kasuwanci ko makamancinsu, a’a, aikin gwamnati shine samarda da yanayin yin kasuwancin ko wasu muhimman harkoki na halas da kuma tsaro dan komi ya tafi daidai.

    Amma yana zama wajibi a wasu lokutan gwamnati ta tsunduma kanta cinki harka musamman idan ta duba cewa jama’arta na da shaawa ko muradin wannan harka amma babu masu gudanarwa ko zuba jari a cikinta.

    Irin wannan dalilinne yasa gwamnatocin kasar nan da dama ke tsuduma cikin harkar mallakar kungoyin wasanni kamar kwallon kafa, kwallon kwando, kwallon raga da sauransu.

    Alal misali a Maiduguri gwamnatin jihar Borno ke daukar nauyin kungiyar kwallon kafa ta El-Kanemi, a jihar Pilato, gwamnatin jihar ke da Plateau United, a jihar Kwara, akwai Kwara United, a jihar Rivers, gwamnatin jiharce ke daukar nauyi Rivers United, sai nan Kano inda gwamnatin jihar Kano ceke  daukar nauyin  kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars haka kuma sauran jahohi.

    Gwamnatocin jahohi na daukar nauyin wadannan kungiyoyin wasanne saboda rashin samun shigar yan kasuwa ko kungiyoyin da ba na gwamnati ba shiga harkar saboda makudan kudin da harkar ke ci sannan kuma babu wata tabbatacciyar riba  a ciki.

    Da akwaimasu daukar nauyin irin wadaannan kungiyoyi, to fa babu yadda gwamnatocin jihohi zasu tsunduma kansu cikin harkar, saidai kallo kawai.

    Don haka tunda a yanzu a Kano an sami mutane daidaiku suna nuna shaawarsu wajen daukan nauyin ko mallakar kungiyoyin wasan kwallon kafa a jihar Kano, to fa zama wajibi ga gwamnatin jiha to fito fili ta taimakawa kungiyoyin don samun nasararsu.

    Wajibcin  hakan ya faru ne saboda damar da yawacin matasan jiharnan suka samu na damar yin wasan a kungiyar Barau ba tare da sun je ko’ina ba.

    Bugu da kari jama’ar gari ma sun sami wata damar na kasha kwarkwatar idanunsu wajen ganin manya kungiyoyin wasan kwallon kafa na wasu jahohi.

    A halin yanzu, matsayin kungiyoyinmu biyu masu daraja, watau Kano Pillars FC da Barau FC dake cikin  gasar Nigeria Premier Football League (NPFL) sun zama abin damuwa ga masoya, ‘yan wasa da masu ruwa da tsaki a harkar wasanni a fadin Jihar Kano da ma kasa baki daya.

    Wadannan kungiyoyi biyu, wadanda a da suke alfahari da daukaka ga jama’ar Kano, yanzu suna fama da rashin nasara tare da kasancewa a kasan teburin gasar, lamarin da ke bukatar gaggawar kulawa daga gwamnati.

    A halin yanzu, rahotanni sun nuna cewa Barau FC na da maki biyar kacal, yayin da Kano Pillars FC ke da  hudu, abin da ke nuni da tabarbarewar da ta samo asali daga rashin kyakkyawar tafiyar da al’amuran gudanarwa da kuma matsalolin fasaha.

    Magoya baya sun dade suna jimami da takaici yayin da suke kallon kungiyoyinsu nata rashin nasara a gasar duk da tarihin Kano na kasancewa cibiyar hazikan ‘yan wasa da kwarewa a harkar kwallon kafa.

    Bincike da lura sun nuna cewa akwai wasu muhimman dalilai da suka haddasa wannan tabarbarewowin:

    1. Rashin Kyakkyawar Gudanarwa: Babu isasshen kulawa da tsari tsakanin shugabancin kungiyoyin da hukumomin gwamnati masu kula da harkar wasanni.
    2. Rashin Kudi da Tsarin Amfani da Albarkatu: Kungiyoyin suna fama da karancin kudi ko kuma rashin tsari wajen kashe kudade, da kuma matsalar kulawa da ‘yan wasa, wanda ke rage musu kwarin gwiwa.
    1. Matsalar Koyarwa da Horarwa: Sauyawa a fannin masu horarwa da rashin tsayayyen tsarin fasaha suna hana kafa daidaitaccen tsari na dogon lokaci.
    1. Rashin Zuba Jari a Matasa: An kasa baiwa matasa dama ta shiga cikin kungiyoyi ta hanyar horarwa daga matakin ƙasa, lamarin da ke sa kungiyoyi su dogara da siyan ‘yan wasa na wucin gadi.
    1. Rashin Tsari da Binciken Ayyuka: Rashin bin diddigin aikace-aikace da rashin gaskiya a cikin tsarin gudanarwa ya jawo watsi da nagarta da sakaci.

    Don dawo da martaba da nasarar kungiyoyin, ina bada wadannan shawarwarin ga Gwamnatin Jihar Kano da masu ruwa da tsaki:

    1. Kafa Kwamitin Bincike Mai ‘Yanci: Gwamnati ta nada kwamitin kwararru da tsofaffin ‘yan wasa, masu gudanarwa, da wakilan magoya baya domin yin cikakken bincike kan yadda ake tafiyar da Pillars da Barau FC.
    1. Yi Binciken Kudi da Gudanarwa: A gudanar da cikakken binciken kudade da tsarin gudanarwa domin gano kura-kurai da daukar matakin gyara.
    1. Tsarin Sabon Gudanarwa: A kafa sabon tsari na gudanarwa wanda zai kasance mai zaman kansa amma na gaskiya da amana, tare da sakamako bisa aiki da nagarta.
    1. Zuba Jari a Matasa da Harkar Gargajiya: A farfado da kungiyoyin matasa da cibiyoyin horaswa domin samar da sabbin ‘yan wasa masu kwarewa daga Kano da kewaye.
    1. Kafa Shugabannin Fasaha Masu Kwarewa: A nada koci da jami’an fasaha masu kwarewa tare da tabbatar da suna da kwangila da sharuddan aiki bisa nasarori.
    1. Gwamnati Ta Kara Kula da Bin Didddigi: Duk da karfafa hadin gwiwar masu zaman kansu, gwamnati ta ci gaba da sa ido don tabbatar da cewa duk kudade da kayan aiki suna zuwa ga manufar ci gaban kungiyoyin.

    Martabar Kano a fagen kwallon kafa tana cikin barazana saboda irin wannan tabarbarewa.

    Lokaci ya yi da Gwamnatin Kano ta dauki mataki cikin gaggawa domin dawo da karfin gwiwa, kwarjini, da sahihancin gudanarwa a Kano Pillars FC da Barau FC.

    Idan aka dauki matakai cikin hikima yanzu, wadannan kungiyoyi za su sake zama tushen farin ciki, hadin kai da ci gaban tattalin arziki ga al’ummar Jihar Kano da Najeriya baki daya.

    Haka kuma yakamata gwamnati ta sani cewa barin su wadannan kungiyoyin a haka babbar illace ga jihar Kano a fagen wasan kwallon kafa.

    A fidda siyasa, a kuma duba jihar Kano da kuma cigaban jihar kawai.

    Barau Dole gwamnati Kano Pillars Kokarin Rashin tayi wani abu
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleSWAN: Genuine sports stakeholder than NFF, other federation members
    Next Article Extortion at Urology Center: Gov Abba must hear this
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Kano Sports: Huge expectations for new Kano Pillars, Sports Commission Boards

    June 29, 2026

    Musbahu, 12 others appointed to manage Kano Pillars Board

    June 26, 2026

    After victory, Kano Pillars Basketball Team turns to Gov. Yusuf for Help

    June 24, 2026

    Blame government for Kano Pillars’ crisis — Zico

    June 23, 2026

    Kano Pillars’ ₦200m debt crisis: Urgent call for Governor Abba’s intervention

    June 23, 2026

    Ahead of New Season: Kano Pillars set to resume training next Monday

    June 5, 2026
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    NASTOCE 2026: Chief Abiodun Odusanwo, Dr. Badaki Aliyu Earn Meritorious Honours

    July 14, 2026

    NFF names Mahmud Hadejia chairman of Beach Soccer, Futsal committee

    July 14, 2026

    New Kano Pillars Management: Any hope for real change?

    July 13, 2026

    Gombe Emir’s Cup: Organisers unveil quarter-final fixtures, match dates

    July 10, 2026

    With full government support, Babangida, Maizare, others must produce results

    July 10, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.