Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Dr. Maizare emerges VP, Karate Federation

      October 26, 2025

      Dala Hard Courts Director elected VP, Nigeria Tennis Federation

      October 26, 2025

      Dala Hard Courts Director elected VP Nigeria Tennis Federation

      October 26, 2025

      Celebrations as SWAN honours Ado Salisu

      October 20, 2025

      Handball: Army massacres Pillars

      October 13, 2025
    • Column

      TSY: Accomplished talent scout, content producer, football agent

      October 27, 2025

      NPFL’s unjust and unfair treatment for Kano Pillars

      October 20, 2025

      On Shehu Adamu’s assessment of Kano Pillars’ poor performance

      October 13, 2025

      SWAN: Genuine sports stakeholder than NFF, other federation members

      October 6, 2025

      Changes in Barau FC: Where DSP Barau Jibrin fumbles

      September 29, 2025
    • News & Media

      Ganduje named Mi-Yetti Allah’s adviser for youth empowerment

      October 25, 2025

      Few minutes in the midst of lawyers

      October 24, 2025

      Tunda Kano Pillars ta nada Babaganaru…

      October 22, 2025

      Re-Extortion at Urology Center: Gov Abba must hear this

      October 10, 2025

      Environmental Journalists begin two-day training in Abuja

      September 23, 2025
    • Analysis

      Matsalar Kano Pillars ibtala’ice, amma…

      October 28, 2025

      Tunda Kano Pillars ta nada Babaganaru…

      October 22, 2025

      Technical Advisor, Assistant for Kano Pillars Suspended: What’s next for Sai Masu Gida?

      October 21, 2025

      Korar Ogenye da Yaro Yaro: Ba su suka kar zomon ba

      October 20, 2025

      Rashin kokarin Kano Pillars da Barau: Sai fa gwamnati ta yi wani abu

      October 7, 2025
    • Personality Profiles

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024

      Dr. Usman Ibrahim Aikawa: New Kano Poly, Director Academic Planning

      January 2, 2024
    Sports Eye
    Home » Matsalar Kano Pillars ibtala’ice, amma…
    Sports Analysis

    Matsalar Kano Pillars ibtala’ice, amma…

    Sani YusifBy Sani YusifOctober 28, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    1a

    A lokacin da wasu tsirari marasa kishin jihar Kano ke murna da farin cikin halin da kungiyar Kwallon kafa ta Kano Pillars ke ciki, wasu da dama na bakin ciki mara misaltuwa da wannan al’amari, kuma na fata da addu’ar ganin karshen wannan yanayin.

    Da yawan masu bakin cikin wannan mummunar halin da Kano Pillars ta sami kanta a ciki na hangen wasu abubuwan da suka zama haddasana ga koma bayan kungiyar.

    Koda yake ba sabon abu bane ganin kungiyar Kano Pillars a baya dumu-dumu a gasar wasan pirimiya ta kasa, amma na wannan lokacin abin yafi muni saboda wasu dalilai.

    Dalilan kuwa sune yadda mahukuntan suka bari mai horarwar kungiyar Usman Abdallah ya subuce a karshen kakar wasa ta bara ba tare dayin saurin maye gurbinsa ba.

    READ ON: Tunda Kano Pillars ta nada Babaganaru…

    Wasu kuma na ganin rashin samo gogaggun yan wasa don cike gurbin wadanda suka gaza ko kuma suka ko koma wasu kungiyoyin shine babban koma bayan da kungiyar ta samu wanda kuma shine ya jawo halinda ake ciki.

    Da yawa kuma na zargin kasancewar kungiyar Kano Pillars karkashin ma’aikatar matasa da wasanni  ba ofishin gwamna ba kamar yadda aka saba.

    Domin tun lokacin da aka kafa kungiyar Kano Pillars a shekarar 1990, ba’a taba ganinta dumu-dumu a karkashin ofishin kwamishina ba irin wannan lokacin.

    Wannan kuwa ya faru ne saboda ba kamar yadda aka saba gani a da ba, yanzu komai daga offishin kwamishina kungiyar take karba.

    Hatta motocin da gwamnatin jiya karkashin Abba Kabir Yusuf ta samawa kungiyar Kano Pillars kwamishinane ya rarraba ba gwamna ba.

    A wannan lokaci duk wasu bukatun kungiyar ta ofishin kwamishina suke fitowa ba daga ofishin gwamna ba, al’amarin da yake damu da daurewa magoya baya da yawa.

    Don nemo hakikanin abubuwan da suka da baibaye kungiyar da kuma samo maganinsu, tsohon mataimakain mai horarda kungiyar Kano Pillars, Nasiru Salisu Rasha ya lissafa abubuwa guda hudu wadanda a ganinsa sune matsalolin kungiyar.

    A cewarsa, matsalar farko a wajen daukar yan wasa take. A ganinsa yakamata a bar mai horarwa ya neme yan wasan da zasuyi masa aiknsa don samun sakammako maikyau. Kowa ya hakura yabar mai horarwa yayi aikinsa don samun nasara.

    A ganinsa aikin shugabannin kungiyar yana wajen fili ne ba cikin fili ba. Jin dadin yan wasa, samarda yanayin walwala ga yan wasa, biyan bonus, kula da lafiyarsu da kuma tabbatarwa kowane dan wasa ya sami hakkinsa sune ayyukan shugabannin kungiyar.

    “Ba aikin hukumar gudanarwa ko manaja bane daukar yan wasa. Wannan aikine na mai horarwa domin shiyasan wanda zai bashi sakammakon da yake so,” cewar Rasha.

    Wani abin da yake komar da kungiyar baya a ganin Nasiru Rasha shine bangaranci wanda idan ba’a soke shiba bazaibar kungiyar ta cigaba ba. Kowa dan unguwarsu kawai yakeso badan wata unguwa ba duk kyawu ko rashin kyawunsa.

    Abu na uku kuma a cewarsa, shine wajen zama na babban bene (VIP stand). A nan ne ake kulla duk wani abu mara kyau.

    Idan cin mutuncin yan kwallo ko mai horarwa ne daga wannan babban benan ake kullo shi. Don ha yake ganin yakamata asan yadda zaayi a rage masu zama a wajen.

    Abu nakarshe a cewar Nasiru Salisu Rasha shine daina sa bakin shugabannin kungiyar wajen yan wasan da yakamata su buga wasa. Su bar mai horarwa ya zabi wadanda zasu bashi sakammako mai kyau.

    Nasiru Rasha ya kuma bada shawarar kafa kotun tafi da gidanka a cikin filin wasan Sani Abacha don hukunta duk wani wanda aka kama da laifin tayarda tarzoma a lokacin wasanni.

    Wadannan a ganinsa sune matsaloli da kuma yadda zaa magance su.

    Bincikena ya kuma nunamin wasu hanyoyi da yakamata abi don gujewa daga irin wannan yanayin kamar haka:-

    1. Gyaran tsarin gudanarwa

    Kano Pillars tana bukatar sabon tsari na shugabanci wanda zai mai da hankali kan gaskiya, tsari da kuma ingantaccen shiri. Dole ne a daina siyasantar da harkar ƙungiyar, a bai wa ƙwararru damar gudanar da ita ba tare da tsangwama daga masu hannu da shuni ko gwamnati ba.

    1. Inganta tsarin koyarwa da horar da ‘yan wasa

    Ƙungiyar tana buƙatar kwararrun masu horarwa (coaches) da suka san dabarun zamani na ƙwallon ƙafa.

    Hakan zai taimaka wajen dawo da dabaru, dabarun tsaron gida (defense organization), da kuma ingantaccen kai hari (attack transition) da kuma cin kwallo (scoring goals).

    1. Gina ‘yan wasa daga matasa

    Maimakon dogaro da yan wasa daga (agents) yakamata Kano Pillars ta mayar da hankali wajen gina matasa masu basira daga makarantu da ƙananan kungiyoyi. Wannan zai sa ƙungiyar ta samu sabbin jini, ƙwarai, da kuzari.

    1. Tallafi da kwanciyar hankali ga ‘yan wasa

    Ƴan wasa suna buƙatar biyan albashi ko bonus a lokaci, da kuma kulawa da su ta fuskar lafiyar jiki da walwala. Idan aka tabbatar da wannan, za su fi sadaukar da kansu wajen kare martabar ƙungiyar.

    1. Taimakon magoya baya da haɗin kai

    Magoya bayan Kano Pillars suna da rawar takawa sosai. Ya kamata su ci gaba da goyon baya cikin lumana, su guji tashin hankali, domin hakan yana sa hukumar ƙwallon ƙafa ta hukunta ƙungiyar, kuma hakan kan haifar da matsin lamba.

    1. Shirin dogon lokaci

    Dole ne ƙungiyar Kano Pillars ta samar da shiri na shekaru 3 zuwa 5, wanda zai kunshi burin dawowa da martabar Pillars, tabbatar da tsayuwa a Premier League, da kuma samun damar fafatawa a CAF competitions.

     

    amma.. ibtala'i ne Matsalolin Pillars
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleTSY: Accomplished talent scout, content producer, football agent
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Tunda Kano Pillars ta nada Babaganaru…

    October 22, 2025

    Technical Advisor, Assistant for Kano Pillars Suspended: What’s next for Sai Masu Gida?

    October 21, 2025

    Korar Ogenye da Yaro Yaro: Ba su suka kar zomon ba

    October 20, 2025

    Handball: Army massacres Pillars

    October 13, 2025

    Rashin kokarin Kano Pillars da Barau: Sai fa gwamnati ta yi wani abu

    October 7, 2025

    Barau FC, please wake up.

    September 15, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Matsalar Kano Pillars ibtala’ice, amma…

    October 28, 2025

    TSY: Accomplished talent scout, content producer, football agent

    October 27, 2025

    Dr. Maizare emerges VP, Karate Federation

    October 26, 2025

    Dala Hard Courts Director elected VP, Nigeria Tennis Federation

    October 26, 2025

    Dala Hard Courts Director elected VP Nigeria Tennis Federation

    October 26, 2025
    © 2025 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.