Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Sports Eye
    SUBSCRIBE
    • Home
    • News

      Backing NFCA on Sports Commissioner appointment, but…

      May 5, 2026

      Kano to Host NSSF/Milo Inter-Secondary Schools Basketball Championship

      May 5, 2026

      Massive prayers turnout for late Lydia Andishu, mother of Abdulgafar Oladimeji

      May 1, 2026

      Tributes continue as Kano SWAN, others mourn Galadima

      April 24, 2026

      CN Yahaya extends Anti-Drug Campaign to Goron Dutse Center via Sports Initiative

      April 23, 2026
    • Column

      Ending unruly conduct among Kano Pillars Fans

      April 27, 2026

      Kano, Nigerian sports mourn the passing of Galadima

      April 20, 2026

      What I left unsaid during my Sports Commission’s visit

      April 13, 2026

      Shehu Dikko’s NFF reform call: Real commitment or mere words?

      April 7, 2026

      Disheartening state of our ex-players: Way forward

      March 30, 2026
    • News & Media

      Sports as Reform: As Kano NDLEA takes Anti-Drug Campaign to Goron Dutse Centre

      April 28, 2026

      International Women’s Day: Women in Hospitality, Tourism celebrate excellence, professionalism

      February 22, 2026

      Kano Football Coaches host Modern Coaching Seminar for members

      January 7, 2026

      Oseni replaces Ramat as NERC chairman after Senate rejection

      December 19, 2025

      Ahned Musa: Honoring 15 Years of Dedication and Selfless Service

      December 17, 2025
    • Analysis

      Alleged Bias in Kano Sports Support: What Kano FA Should Address

      May 5, 2026

      As Pillars crash out of Federation Cup, focus turns to NPFL survival

      April 27, 2026

      Jamilu Uba’s case for stronger protection of Match Officials

      April 27, 2026

      Late Ibrahim Galadima, MFR: The Man

      April 22, 2026

      Late Galadima: Voices from sports community

      April 22, 2026
    • Personality Profiles

      Muhammad Wasilu Kawo: New Nasara Radio Program Manager

      December 19, 2025

      Alhaji Shehu Muhammad Dankadai, Sarkin Shanun Kano

      October 28, 2024

      Engr. Ibrahim Usman Aikawa: New Kano Poly Governing Council’s PAB’s representative

      August 24, 2024

      Aminu Kano 40 years after…

      April 17, 2024

      Ameh Agnes: A woman farmer of repute

      April 15, 2024
    • Advert Rates
    Sports Eye
    Home » Matsalar Kano Pillars ibtala’ice, amma…
    Sports Analysis

    Matsalar Kano Pillars ibtala’ice, amma…

    Sani YusifBy Sani YusifOctober 28, 2025
    Facebook Twitter WhatsApp Email Telegram
    1a

    A lokacin da wasu tsirari marasa kishin jihar Kano ke murna da farin cikin halin da kungiyar Kwallon kafa ta Kano Pillars ke ciki, wasu da dama na bakin ciki mara misaltuwa da wannan al’amari, kuma na fata da addu’ar ganin karshen wannan yanayin.

    Da yawan masu bakin cikin wannan mummunar halin da Kano Pillars ta sami kanta a ciki na hangen wasu abubuwan da suka zama haddasana ga koma bayan kungiyar.

    Koda yake ba sabon abu bane ganin kungiyar Kano Pillars a baya dumu-dumu a gasar wasan pirimiya ta kasa, amma na wannan lokacin abin yafi muni saboda wasu dalilai.

    Dalilan kuwa sune yadda mahukuntan suka bari mai horarwar kungiyar Usman Abdallah ya subuce a karshen kakar wasa ta bara ba tare dayin saurin maye gurbinsa ba.

    READ ON: Tunda Kano Pillars ta nada Babaganaru…

    Wasu kuma na ganin rashin samo gogaggun yan wasa don cike gurbin wadanda suka gaza ko kuma suka ko koma wasu kungiyoyin shine babban koma bayan da kungiyar ta samu wanda kuma shine ya jawo halinda ake ciki.

    Da yawa kuma na zargin kasancewar kungiyar Kano Pillars karkashin ma’aikatar matasa da wasanni  ba ofishin gwamna ba kamar yadda aka saba.

    Domin tun lokacin da aka kafa kungiyar Kano Pillars a shekarar 1990, ba’a taba ganinta dumu-dumu a karkashin ofishin kwamishina ba irin wannan lokacin.

    Wannan kuwa ya faru ne saboda ba kamar yadda aka saba gani a da ba, yanzu komai daga offishin kwamishina kungiyar take karba.

    Hatta motocin da gwamnatin jiya karkashin Abba Kabir Yusuf ta samawa kungiyar Kano Pillars kwamishinane ya rarraba ba gwamna ba.

    A wannan lokaci duk wasu bukatun kungiyar ta ofishin kwamishina suke fitowa ba daga ofishin gwamna ba, al’amarin da yake damu da daurewa magoya baya da yawa.

    Don nemo hakikanin abubuwan da suka da baibaye kungiyar da kuma samo maganinsu, tsohon mataimakain mai horarda kungiyar Kano Pillars, Nasiru Salisu Rasha ya lissafa abubuwa guda hudu wadanda a ganinsa sune matsalolin kungiyar.

    A cewarsa, matsalar farko a wajen daukar yan wasa take. A ganinsa yakamata a bar mai horarwa ya neme yan wasan da zasuyi masa aiknsa don samun sakammako maikyau. Kowa ya hakura yabar mai horarwa yayi aikinsa don samun nasara.

    A ganinsa aikin shugabannin kungiyar yana wajen fili ne ba cikin fili ba. Jin dadin yan wasa, samarda yanayin walwala ga yan wasa, biyan bonus, kula da lafiyarsu da kuma tabbatarwa kowane dan wasa ya sami hakkinsa sune ayyukan shugabannin kungiyar.

    “Ba aikin hukumar gudanarwa ko manaja bane daukar yan wasa. Wannan aikine na mai horarwa domin shiyasan wanda zai bashi sakammakon da yake so,” cewar Rasha.

    Wani abin da yake komar da kungiyar baya a ganin Nasiru Rasha shine bangaranci wanda idan ba’a soke shiba bazaibar kungiyar ta cigaba ba. Kowa dan unguwarsu kawai yakeso badan wata unguwa ba duk kyawu ko rashin kyawunsa.

    Abu na uku kuma a cewarsa, shine wajen zama na babban bene (VIP stand). A nan ne ake kulla duk wani abu mara kyau.

    Idan cin mutuncin yan kwallo ko mai horarwa ne daga wannan babban benan ake kullo shi. Don ha yake ganin yakamata asan yadda zaayi a rage masu zama a wajen.

    Abu nakarshe a cewar Nasiru Salisu Rasha shine daina sa bakin shugabannin kungiyar wajen yan wasan da yakamata su buga wasa. Su bar mai horarwa ya zabi wadanda zasu bashi sakammako mai kyau.

    Nasiru Rasha ya kuma bada shawarar kafa kotun tafi da gidanka a cikin filin wasan Sani Abacha don hukunta duk wani wanda aka kama da laifin tayarda tarzoma a lokacin wasanni.

    Wadannan a ganinsa sune matsaloli da kuma yadda zaa magance su.

    Bincikena ya kuma nunamin wasu hanyoyi da yakamata abi don gujewa daga irin wannan yanayin kamar haka:-

    1. Gyaran tsarin gudanarwa

    Kano Pillars tana bukatar sabon tsari na shugabanci wanda zai mai da hankali kan gaskiya, tsari da kuma ingantaccen shiri. Dole ne a daina siyasantar da harkar ƙungiyar, a bai wa ƙwararru damar gudanar da ita ba tare da tsangwama daga masu hannu da shuni ko gwamnati ba.

    1. Inganta tsarin koyarwa da horar da ‘yan wasa

    Ƙungiyar tana buƙatar kwararrun masu horarwa (coaches) da suka san dabarun zamani na ƙwallon ƙafa.

    Hakan zai taimaka wajen dawo da dabaru, dabarun tsaron gida (defense organization), da kuma ingantaccen kai hari (attack transition) da kuma cin kwallo (scoring goals).

    1. Gina ‘yan wasa daga matasa

    Maimakon dogaro da yan wasa daga (agents) yakamata Kano Pillars ta mayar da hankali wajen gina matasa masu basira daga makarantu da ƙananan kungiyoyi. Wannan zai sa ƙungiyar ta samu sabbin jini, ƙwarai, da kuzari.

    1. Tallafi da kwanciyar hankali ga ‘yan wasa

    Ƴan wasa suna buƙatar biyan albashi ko bonus a lokaci, da kuma kulawa da su ta fuskar lafiyar jiki da walwala. Idan aka tabbatar da wannan, za su fi sadaukar da kansu wajen kare martabar ƙungiyar.

    1. Taimakon magoya baya da haɗin kai

    Magoya bayan Kano Pillars suna da rawar takawa sosai. Ya kamata su ci gaba da goyon baya cikin lumana, su guji tashin hankali, domin hakan yana sa hukumar ƙwallon ƙafa ta hukunta ƙungiyar, kuma hakan kan haifar da matsin lamba.

    1. Shirin dogon lokaci

    Dole ne ƙungiyar Kano Pillars ta samar da shiri na shekaru 3 zuwa 5, wanda zai kunshi burin dawowa da martabar Pillars, tabbatar da tsayuwa a Premier League, da kuma samun damar fafatawa a CAF competitions.

     

    amma.. ibtala'i ne Matsalolin Pillars
    Share. Facebook Twitter Telegram Email WhatsApp Copy Link
    Previous ArticleTSY: Accomplished talent scout, content producer, football agent
    Next Article Kidney Patients send SOS to Governor AKY
    Sani Yusif
    • Website

    I was a staff of the then Triumph Newspapers, with keen interest in sports journalism which drove me to the unit where I was supported and oiled in the dynamics of modern sports reporting by my mentor/friend, Sani Zaria, the then Group Sports Editor of the Triumph. And when he left in 1995, I tried to sustain the spirit against all odds with a column sportesye. But when The Triumph was closed, I was moved to Kano Polytechnic as a lecturer until my retirement last 3 years, which gives me time to return to what I know best , the recreation of the SPORTS EYE.

    Related Posts

    Alleged Bias in Kano Sports Support: What Kano FA Should Address

    May 5, 2026

    As Pillars crash out of Federation Cup, focus turns to NPFL survival

    April 27, 2026

    Jamilu Uba’s case for stronger protection of Match Officials

    April 27, 2026

    Late Ibrahim Galadima, MFR: The Man

    April 22, 2026

    Late Galadima: Voices from sports community

    April 22, 2026

    Sani Zaria’s tribute to Late Galadima: Honouring a lasting Legacy

    April 20, 2026
    Add A Comment

    Comments are closed.

    Stay In Touch
    • Facebook
    • Twitter
    • Pinterest
    • Instagram
    • YouTube
    • Vimeo
    Latest Posts

    Alleged Bias in Kano Sports Support: What Kano FA Should Address

    May 5, 2026

    Backing NFCA on Sports Commissioner appointment, but…

    May 5, 2026

    Kano to Host NSSF/Milo Inter-Secondary Schools Basketball Championship

    May 5, 2026

    Massive prayers turnout for late Lydia Andishu, mother of Abdulgafar Oladimeji

    May 1, 2026

    Abdalla U. Adamu @ 70: A mentor, brother, father figure

    April 30, 2026
    © 2026 Sports Eye. Redesigned by ENGRMKS & CO..
    • Home
    • About
    • Contact
    • Advert Rates
    • Privacy Policy

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.